Aionian Verses
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol )
(parallel missing)
Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol )
(parallel missing)
In kun ɗauki wannan daga wurina shi ma wani abu ya same shi, za ku kawo furfura kaina zuwa kabari cikin baƙin ciki.’ (Sheol )
(parallel missing)
ya ga cewa saurayin ba ya nan, zai mutu. Bayinka za su sa bawanka, mahaifinmu, yă mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. (Sheol )
(parallel missing)
Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
(parallel missing)
Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
(parallel missing)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol )
(parallel missing)
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol )
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
(parallel missing)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol )
(parallel missing)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol )
(parallel missing)
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
(parallel missing)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
(parallel missing)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol )
(parallel missing)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
(parallel missing)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
(parallel missing)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
(parallel missing)
Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol )
(parallel missing)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
(parallel missing)
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
(parallel missing)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
(parallel missing)
domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol )
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
(parallel missing)
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
(parallel missing)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol )
(parallel missing)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
(parallel missing)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
(parallel missing)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
(parallel missing)
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
(parallel missing)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
(parallel missing)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
(parallel missing)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
(parallel missing)
Za su ce, “Kamar yadda mutum kan yi huda yă tsage ƙasa, haka aka watsar da ƙasusuwanmu a bakin kabari.” (Sheol )
(parallel missing)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
(parallel missing)
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
(parallel missing)
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )
(parallel missing)
Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol )
(parallel missing)
Mutuwa da Hallaka suna nan a fili a gaban Ubangiji, balle fa zukatan mutane! (Sheol )
(parallel missing)
Hanyar rai na yin jagora ya haura wa masu hikima don ta kiyaye shi daga gangarawa zuwa kabari. (Sheol )
(parallel missing)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
(parallel missing)
Mutuwa da Hallaka ba sa ƙoshi, haka idanun mutum ba sa ƙoshi da gani. (Sheol )
(parallel missing)
Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol )
(parallel missing)
Duk abin da hannunka yake yi, ka yi shi da dukan ƙarfinka, gama a cikin kabari in da za ka, babu aiki ko shirye-shirye, ko sani, ko hikima. (Sheol )
(parallel missing)
Ka sa ni kamar hatimi a zuciyarka, kamar hatimi a hannunka; gama ƙauna tana da ƙarfi kamar mutuwa, kishinta yana kamar muguntar kabari, yana ƙuna kamar wuta mai ci, kamar gagarumar wuta. (Sheol )
(parallel missing)
Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol )
(parallel missing)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol )
(parallel missing)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol )
(parallel missing)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol )
(parallel missing)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol )
(parallel missing)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
(parallel missing)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
(parallel missing)
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
(parallel missing)
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
(parallel missing)
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
(parallel missing)
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol )
(parallel missing)
Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol )
(parallel missing)
Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol )
(parallel missing)
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol )
(parallel missing)
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol )
(parallel missing)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
(parallel missing)
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol )
(parallel missing)
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol )
(parallel missing)
ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
(parallel missing)
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna )
but I say unto you, That every man who is angry with his brother without cause, shall be liable to the judgment: and whosoever shall say to his brother, Raca, shall be liable to the sanhedrim: but whosever shall say, Thou fool, shall be liable to be cast into hell fire. (Geenna )
In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
If then thine eye, the right, leads thee to offend, pluck it out, and cast it from thee: for it is highly for thy advantage, that one of thy members be destroyed, and not that thy whole body should be cast into hell. (Geenna )
In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
And if thy right hand leads thee to offend, cut it off, and cast it from thee: for it is highly thy interest that one of thy members should be destroyed, and not that thy whole body should be cast into hell. (Geenna )
Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna )
And be not afraid of those who kill the body, and cannot kill the soul: but fear him rather who is able to destroy both soul and body in hell. (Geenna )
Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. (Hadēs )
And thou, Capernaum, who hast been exalted unto heaven, shalt be cast down to hell: for if the miracles which have been wrought in thee had been done in Sodom, it had remained unto this day. (Hadēs )
Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
And whosoever may speak a word against the Son of man, it shall be forgiven him: but whosoever shall speak against the Holy Ghost, it shall not be forgiven him, neither in this world, nor in the world to come. (aiōn )
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
But the sown among the thorns, is he who heareth the word, and the anxiety about this world and the deceitfulness of riches, choketh the word, and it becometh unfruitful. (aiōn )
abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
the enemy who sowed them is the devil; the harvest is the end of the world; and the reapers are the angels. (aiōn )
“Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
As therefore the zizane are gathered, and burned in the fire; just so shall it be at the end of this world. (aiōn )
Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
Just so shall it be at the end of this world: the angels shall go forth, and shall separate the wicked from amidst the just, (aiōn )
Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
And I tell thee, That thou art Peter, and upon this rock will I build my church, and the gates of hell shall not prevail against it. (Hadēs )
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios )
If then thy hand, or thy foot, lead thee to offend, cut them off, and cast them from thee: for it were better for thee to enter into life, halting or maimed, than having two hands or two feet to be cast into the fire, which is eternal. (aiōnios )
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna )
And if thine eye lead thee to offend, pluck it out and cast it from thee, for it were better for thee to enter into life with one eye only, than having two eyes to be cast into hell-fire. (Geenna )
To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
And lo! a person coming to him, said, Good Master, what good thing shall I do, in order to attain eternal life? (aiōnios )
Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
And every one who hath left family, or brethren, or sisters, or father, or mother, or wife, or children, or lands, for my name sake, shall receive an hundred fold, and shall inherit life eternal. (aiōnios )
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn )
and seeing a fig-tree at the road side, he went up to it, and found nothing on it but leaves only: and saith unto it, Let no fruit spring from thee henceforth for ever: and immediately the fig-tree withered entirely away. (aiōn )
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna )
Wo unto you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye compass sea and land to make one proselyte; and when he is gained, ye make him doubly more the child of hell than yourselves. (Geenna )
“Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna )
Ye serpents, ye broods of vipers! how can ye escape from the damnation of hell? (Geenna )
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
Then as he was sitting upon the mount of Olives, his disciples came to him privately, saying, Tell us, when shall there things be? and what is the sign of thy coming, and of the consummation of the age? (aiōn )
“Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios )
Then shall he say also to those on the left hand, Depart from me, ye cursed, into everlasting fire, prepared for the devil and his angels: (aiōnios )
“Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios )
And these shall go away into everlasting punishment: but the righteous into life eternal. (aiōnios )
kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn )
teaching them to observe all things whatsoever I have commanded you: and, lo! I am with you at all times even to the end of the world. Amen. (aiōn )
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn , aiōnios )
but whosoever shall blaspheme against the Holy Ghost, hath no forgiveness to eternity, but is adjudged to everlasting damnation. (aiōn , aiōnios )
amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
but the anxious cares of this world, and the seducing nature of wealth, and inordinate desires after other things entering in, choke the word, and it becometh unfruitful. (aiōn )
In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
And if thy hand cause thee to offend, cut it off: it were better for thee to enter into life maimed, than having both hands to go into hell, into the fire that never will be quenched: (Geenna )
In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
And if thy foot cause thee to offend, cut it off: it is better for thee to enter into life halting, than having both feet to be cast into hell, into the fire which never can be quenched: (Geenna )
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
And if thine eye cause thee to offend, pluck it out: it is better for thee to enter into the kingdom of God with one eye, than having two eyes to be cast into the fire of hell: (Geenna )
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And as he went out to the road, a person ran to him, and kneeling down, asked him, Good Master, what shall I do that I may inherit eternal life? (aiōnios )
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
who shall not receive an hundred-fold more now, at this very time, houses, and brethren, and sisters, and mothers, and children, and lands, with persecution, and in the world to come life everlasting. (aiōn , aiōnios )
Sai ya ce wa itacen, “Kada kowa yă ƙara cin’ya’yanka.” Almajiransa kuwa suka ji ya faɗi haka. (aiōn )
And Jesus spake and said to it, Let no man eat fruit from thee henceforth for ever. And his disciples heard him. (aiōn )
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
and he shall reign over the house of Jacob for ever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn )
Luke 1:54
(parallel missing)
He hath succoured Israel his servant, that he might be mindful of mercy for ever; (aiōn )
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
(parallel missing)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
as he spake by the mouth of his holy prophets, which have been from the beginning: (aiōn )
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos )
And he besought him that he would not order them to go into the abyss. (Abyssos )
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
And thou Capernaum, which hast been lifted up to heaven, shalt be cast down to hell. (Hadēs )
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And, behold, a certain doctor of the law arose, to make trial of him, saying, Master, by doing what shall I inherit eternal life? (aiōnios )
Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna )
But I will point out to you, whom ye should fear: Fear him, who, after he hath killed, hath power to cast into hell; yea, I say unto you, Fear him! (Geenna )
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn )
And the master praised the unjust steward, because he had acted providently: for the children of this world are more provident among their own generation of men, than the children of light. (aiōn )
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios )
And I say unto you, Make yourselves friends with the unrighteous mammon that when ye fail, they may receive you into the eternal mansions. (aiōnios )
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs )
and in hell, lifting up his eyes, being in torments, he seeth Abraham at a vast distance, and Lazarus in his bosom. (Hadēs )
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And a certain ruler asked him, saying, Good Master, by doing what shall I inherit eternal life? (aiōnios )
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn , aiōnios )
who shall not receive back manifold more in this present time, and in the world to come life everlasting. (aiōn , aiōnios )
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn )
And Jesus in reply said to them, The children of this world marry, and are given in marriage: (aiōn )
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn )
but they who are counted worthy to attain to that world, and the resurrection of the dead, neither marry, nor are given in marriage: (aiōn )
don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios )
that every one who believeth on him may not perish, but have life eternal. (aiōnios )
Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios )
For God so loved the world, that he gave his only begotten Son, that every one who believeth in him should not perish, but have life eternal. (aiōnios )
Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios )
He that believeth on the Son hath life eternal: and he that believeth not on the Son shall not see life: but the wrath of God abideth upon him. (aiōnios )
amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
but whosoever shall drink of the water which I shall give him, he shall no more thirst to eternity; but the water which I will give him, shall be in him a fountain of water springing up to life eternal. (aiōn , aiōnios )
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
And he that reapeth receiveth wages, and gathereth fruit unto life eternal: that both he that soweth and he that reapeth may rejoice together. (aiōnios )
“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Verily, verily, I say unto you, That he that heareth my word, and believeth on him that sent me, hath everlasting life, and shall not come into judgment; but is passed from death into life. (aiōnios )
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
Search the scriptures; for ye suppose in them ye have eternal life: and these are they which testify of me. (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
Labour not for the meat which is perishable, but for that meat which endureth unto life eternal, which the Son of man will give you: for him hath the Father sealed, even God. (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
And this is the will of him that sent me, That every one who seeth the Son, and believeth on him, should have life eternal: and I will raise him up at the last day. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
Verily, verily, I say unto you, He that believeth on me hath everlasting life. (aiōnios )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
I am the bread that giveth life, which came down from heaven: if any person eat of this bread, he shall live to eternity; and the bread indeed which I shall give is my flesh, which I will give for the life of the world. (aiōn )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
He that eateth my flesh, and drinketh my blood, hath life eternal: and I will raise him up at the last day. (aiōnios )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
This is the bread which came down from heaven, not as the manna your fathers did eat, and died: he that eateth this bread shall live to eternity. (aiōn )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
Then Simon Peter answered him, Lord, unto whom shall we go from thee? thou hast the words of eternal life. (aiōnios )
Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn )
But the slave abideth not in the family for ever: but the son abideth for ever. (aiōn )
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn )
Verily, verily, I say unto you, If any man observe my saying, he shall never see death to all eternity. (aiōn )
Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn )
Then said the Jews to him, Now we know that thou hast a devil. Abraham is dead, and the prophets; and thou sayest, If any man observe my word, he shall never taste of death to eternity. (aiōn )
Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
From the creation of the world hath it never been heard, that any man opened the eyes of one born blind. (aiōn )
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
and I give unto them everlasting life and they shall never perish to eternity, and no person shall pluck them out of my hand. (aiōn , aiōnios )
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn )
and every one who is alive, and believeth in me, shall never die to eternity. Believest thou this? (aiōn )
Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios )
He that loveth his life shall lose it; and he that hateth his life in this world, shall preserve it to life eternal. (aiōnios )
Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn )
Then the multitude answered him, We have heard out of the law, that the Messiah abideth for ever: and how sayest thou, That the Son of man must be lifted up? who is this Son of man? (aiōn )
Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios )
And I know that his commandment is life eternal: therefore the things which I speak to you, just as the Father spake to me, so speak I. (aiōnios )
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
Peter saith to him, Thou shalt never wash my feet: no, never. Jesus answered him, Except I wash thee, thou hast no part with me. (aiōn )
Zan kuwa roƙi Uba, zai kuwa ba ku wani Mai Taimakon da zai kasance tare da ku har abada, (aiōn )
And I will ask the Father, and he shall give you another Comforter, that he may abide with you for ever; (aiōn )
Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios )
even as thou hast given him authority over all flesh, that with regard to all those whom thou hast given him, he should give to them eternal life: (aiōnios )
Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios )
and this is eternal life, that they should know thee the only true God, and him whom thou hast sent, Jesus, the Messiah. (aiōnios )
gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
that thou wilt not leave my soul in the mansion of the dead, nor permit that Holy One of thine to see corruption. (Hadēs )
Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
he, foreseeing this, spake of the resurrection of the Messiah, that his soul should not be left in the mansion of the dead, and that his flesh should not see corruption. (Hadēs )
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
whom the heaven indeed must receive, until the times of restoration of all things, which God hath spoken of by the mouth of all his holy prophets from the beginning of the world. (aiōn )
Sai Bulus da Barnabas suka amsa musu gabagadi, suka ce, “Ya zama mana dole mu yi muku maganar Allah da farko. Da yake kun ƙi ta ba ku kuma ga kun cancanci rai madawwami ba, to, za mu juya ga Al’ummai. (aiōnios )
Then Paul and Barnabas speaking with undaunted boldness, said, It was necessary that the word of God should be first spoken unto you: but since ye have thrust it from you, and judged yourselves not worthy of eternal life, lo! we turn to the Gentiles. (aiōnios )
Sa’ad da Al’ummai suka ji haka, sai suka yi farin ciki suka ɗaukaka maganar Ubangiji; kuma duk waɗanda aka zaɓa don samun rai madawwami, suka gaskata. (aiōnios )
Now when the Gentiles heard this, they rejoiced, and glorified the word of the Lord: and they believed, even as many as were ordained to life eternal. (aiōnios )
da aka sani tun zamanai. (aiōn )
Known unto God from the beginning are all his works. (aiōn )
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios )
For from the creation of the world his invisible perfections, discoverable in the works that are made, are clearly seen, even his eternal power and deity; so that they are inexcusable: (aïdios )
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn )
who perverted the truth of God by falsehood, and worshipped and paid divine honours to the thing created instead of the Creator, who is blessed for evermore. Amen. (aiōn )
Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. (aiōnios )
to those who, in the patient practice of good works, seek glory and honour and immortality―eternal life. (aiōnios )
domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios )
that as sin had reigned by death, even so might grace reign through righteousness unto life eternal by Jesus Christ our Lord. (aiōnios )
Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios )
But now being set at liberty from sin, and become servants to God, ye have your fruit unto holiness, and at the end life eternal. (aiōnios )
Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios )
For the wages of sin is death; but the gift of God is life eternal in Jesus Christ our Lord. (aiōnios )
Kakannin-kakannin nan kuma nasu ne, Kiristi kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo ya tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome! Amin. (aiōn )
of whom are the fathers, and from whom as respecting the flesh Christ sprung, who is over all, the blessed God for evermore. Amen. (aiōn )
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos )
or, Who shall descend into the abyss?” (that is, to bring Christ up again from the dead.) (Abyssos )
Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē )
For God hath shut up all in unbelief, that he might have mercy upon all. (eleēsē )
Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn )
Because by him, and through him, and for him, are all things, to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
Kada ku ci gaba da yin abin da duniya take yi, sai dai ku bar halinku ya sāke, ta wurin sabunta hankalinku ɗungum, don ku tabbatar da abin da Allah yake so yake, abu mai kyau, mai daɗi da kuma cikakke. (aiōn )
And be not conformed to this world, but be transformed by the renovation of your mind, that you may prove by experience what is the will of God, that is good, acceptable, and perfect. (aiōn )
Ɗaukaka ta tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa’azin Yesu Kiristi, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil azal, (aiōnios )
Now to him that is able to stablish you according to my gospel, and the preaching of Jesus Christ, agreeable to the revelation of the mystery; which was concealed from all former ages, (aiōnios )
amma yanzu kuwa aka bayyana, aka kuma sanar ta wurin rubuce-rubucen annabawa bisa ga umarnin Allah madawwami, domin dukan al’ummai su gaskata su kuma yi masa biyayya (aiōnios )
but is now made manifest, and by the prophetical scriptures, according to the commandment of the eternal God, notified to all the Gentiles to bring them to the obedience of faith: (aiōnios )
ɗaukaka ta tabbata har abada ga Allah, wanda shi ne kaɗai mai hikima ta wurin Yesu Kiristi! Amin. (aiōn )
to the only wise God, through Jesus Christ, be glory for ever and ever. Amen. Written to the Romans, and sent by Phoebe, a deaconess of the church in Cenchrea. (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
Where is the sophist? where is the scribe? where is the inquisitive searcher after this world’s wisdom? hath not God turned into folly the wisdom of this world? (aiōn )
Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. (aiōn )
But we speak wisdom among the perfect: yet not the wisdom of this world, nor of the rulers of this world, who are destroying themselves: (aiōn )
A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. (aiōn )
but we speak the wisdom of God, which had been hid in mystery, which God predestined before the worlds were, for our glory: (aiōn )
Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. (aiōn )
which none of the rulers of this world have known: for if they had known it, they would not have crucified the Lord of glory. (aiōn )
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
Let no man deceive himself. If any man among you thinketh himself a wise man in this world, let him become a fool, that he may be wise. (aiōn )
Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe. (aiōn )
Wherefore if meat give occasion of offence to my brother, I will in no wise eat meat for ever, that I give no cause of offence to my brother. (aiōn )
Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn )
Now all these things happened unto them as examples, but they are written for our admonition, on whom the ends of the ages are come. (aiōn )
“Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
O death, where is thy sting? O grave, where is thy victory? (Hadēs )
Allahn zamanin nan ya makanta hankulan marasa ba da gaskiya, yadda har ba za su iya ganin hasken bishara ta ɗaukakar Kiristi ba, wanda yake kamannin Allah. (aiōn )
among whom the god of this world hath blinded the minds of the unbelievers, that the light of the gospel of the glory of Christ, who is the image of God, should not dart its bright beams upon them. (aiōn )
Don wannan’yar wahalar tamu mai saurin wucewa, ita take tanadar mana madawwamiyar ɗaukaka mai yawa, fiye da kwatanci. (aiōnios )
For our momentary light affliction worketh for us a transcendently far more exceeding eternal weight of glory; (aiōnios )
Domin ba abubuwan da ido yake gani ne muke dubawa ba, sai dai marasa ganuwa. Gama abubuwan da ake gani masu saurin wucewa ne, marasa ganuwa kuwa, madawwama ne. (aiōnios )
whilst we direct our aim not to the things which are seen, but to the things which are not seen: for the things which are seen are temporary, but the things that are not seen are eternal. (aiōnios )
Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios )
FOR we know that if our earthly house of this tabernacle should be taken down, we have a building from God, a house not made with hands, eternal in the heavens. (aiōnios )
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ya ba gajiyayyu hannu sake, ayyukansa na alheri madawwama ne.” (aiōn )
as it is written, “He hath scattered abroad, he hath given to the poor, his righteousness abideth for ever.” (aiōn )
Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn )
The God and Father of our Lord Jesus Christ, who is blessed for evermore, knoweth that I lie not. (aiōn )
Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
who gave himself for our sins, that he might pluck us out of this present wicked world, according to the will of God and our Father: (aiōn )
a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
Wanda ya yi shuki don yă gamshi mutuntakarsa, daga wannan mutuntaka zai girbi hallaka. Wanda ya yi shuki domin yă gamshi Ruhu, daga Ruhu zai girbi rai madawwami. (aiōnios )
For he that soweth unto his flesh, shall of the flesh reap corruption, and he that soweth to the Spirit, shall of the Spirit reap life everlasting. (aiōnios )
Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn )
far above all principality, and authority, and power, and dominion, and every name that is named, not only in this world, but also in that which is to come; (aiōn )
Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn )
wherein in times past ye walked after the fashion of this world, after the prince of the power of the air, the spirit who now worketh with energy in the children of disobedience: (aiōn )
Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn )
That he might shew forth in the ages to come the transcendent riches of his grace, in the kindness shewed to us in Christ Jesus. (aiōn )
An zaɓe ni in bayyana wa dukan mutane shirin asirin nan wanda Allah, mahaliccin kome, ya ɓoye shekara da shekaru. (aiōn )
and to make all men see what the communication of that mystery means, which was hid from the beginning in God, who created all things by Jesus Christ: (aiōn )
Wannan shi ne madawwamin shirinsa, kuma an aikata shi ta wurin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōn )
according to the purpose from everlasting, which he formed in Christ Jesus our Lord: (aiōn )
Bari ɗaukaka ta tabbata a gare shi a cikin ikkilisiya da kuma a cikin Kiristi Yesu, har yă zuwa dukan zamanai, har abada abadin! Amin. (aiōn )
to him be glory in the church, in Christ Jesus, unto all generations for ever and ever. Amen. (aiōn )
Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. (aiōn )
For our conflict is not merely against flesh and blood, but against principalities, and against powers, and against the rulers of the darkness of this world, and against wicked spirits in the aerial regions. (aiōn )
Ɗaukaka ta tabbata ga Allahnmu da Ubanmu har abada abadin. Amin. (aiōn )
Now to God, even our Father, be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn )
the mystery which was hid from ages and from generations, but is now unveiled to his saints; (aiōn )
Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios )
who shall receive punishment, even eternal perdition, from the presence of the Lord, and from the glory of his power: (aiōnios )
Ubangijinmu Yesu Kiristi kansa da kuma Allah Ubanmu, wanda ya ƙaunace mu kuma ta wurin alherinsa yă ba mu madawwamiyar ƙarfafawa da kyakkyawar bege, (aiōnios )
Now our Lord Jesus Christ himself, and our God, and Father, who hath loved us, and given us everlasting consolation, and good hope through grace, (aiōnios )
Amma saboda wannan dalilin ne aka nuna mini jinƙai domin ta wurina, mafi zunubi duka, Kiristi Yesu yă iya bayyana matuƙar haƙurinsa a matsayin misali ga waɗanda za su gaskata shi su kuma sami rai madawwami. (aiōnios )
But for this end obtained I mercy, that in me, the chief, Jesus Christ might shew forth all long-suffering, for a pattern to those who should after believe in him unto eternal life. (aiōnios )
Bari girma da ɗaukaka su tabbata har abada abadin ga Sarki madawwami, wanda ba ya mutuwa, wanda ba a ganinsa, wanda kuma shi ne kaɗai Allah! Amin. (aiōn )
Now to the king eternal, immortal, invisible, the only wise God, be honour and glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios )
Strain every nerve in the noble conflict of faith, lay fast hold on eternal life, unto which also thou hast been called, and hast confessed the good confession before many witnesses. (aiōnios )
wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios )
who alone possesseth immortality, inhabiting light inaccessible, whom no man hath seen, nor can see: to whom be honour and glory eternal. Amen. (aiōnios )
Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn )
Charge the rich in this world not to be lifted up with pride, nor to trust on the stability of wealth, but on the living God, who giveth us richly all things for our enjoyment; (aiōn )
wanda ya cece mu ya kuma kira mu ga rayuwar tsarki ba saboda wani abin da muka yi ba sai dai saboda nufinsa da kuma alherinsa. An ba mu wannan alheri cikin Kiristi Yesu tun fil azal, (aiōnios )
who hath saved us, and called us with an holy calling, not according to our works, but according to his own purpose and grace, which was given us in Christ Jesus before time had a beginning; (aiōnios )
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
Therefore I endure all things for the sake of the elect, that they also may obtain the salvation which is in Jesus Christ with eternal glory. (aiōnios )
gama Demas, saboda ƙaunar wannan duniya, ya yashe ni ya tafi Tessalonika. Kirssens ya tafi Galatiya, Titus kuwa ya tafi Dalmatiya. (aiōn )
for Demas hath forsaken me, having loved this present world, and is gone unto Thessalonica; Crescens to Galatia; Titus to Dalmatia. (aiōn )
Ubangiji zai cece ni daga kowane mugun hari yă kuma kai ni mulkinsa na sama lafiya. A gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
And the Lord will deliver me from every evil work, and preserve me for his celestial kingdom: to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, (aiōnios )
in hope of life eternal, which God, who cannot lie, hath promised before time had a being; (aiōnios )
Yana koya mana mu ce, “A’a” ga rashin tsoron Allah da kuma sha’awace-sha’awacen duniya, mu kuma yi rayuwa ta kamunkai, ta adalci da kuma ta tsoron Allah a cikin wannan zamani, (aiōn )
instructing us, that denying ungodliness and worldly affections, we should live soberly and righteously, and godly in the present day; (aiōn )
wannan fa domin an kuɓutar da mu ne ta wurin alherinsa, don mu zama magāda masu begen ga rai madawwami. (aiōnios )
that justified by his grace, we might become heirs in hope of eternal life. (aiōnios )
Wataƙila abin da ya sa aka raba ka da shi na ɗan lokaci ƙanƙani shi ne don ka same shi da amfani (aiōnios )
For to this end perhaps was he separated from thee for a season, that thou mightest receive him for ever; (aiōnios )
amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
in these last days hath spoken to us by a Son, whom he hath appointed heir of all things, by whom also he made the worlds; (aiōn )
Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
But to the Son, “Thy throne, O God, is unto eternity; a sceptre of rectitude is the sceptre of thy kingdom. (aiōn )
Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
As he saith also in another passage, “Thou art priest forever after the order of Melchisedec;” (aiōn )
kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios )
and complete himself, he became the author of eternal salvation to all who obey him; (aiōnios )
Kuma bai kamata mu ci gaba da koyar da umarnai game da baftisma, ɗibiya hannuwa, tashin matattu, da kuma madawwamin hukunci ba. (aiōnios )
of the doctrine of ablutions, and of imposition of hands, and of the resurrection of the dead, and of eternal judgment. (aiōnios )
waɗanda suka ɗanɗana daɗin maganar Allah da kuma ikokin zamani mai zuwa, (aiōn )
and have tasted the good word of God, and the powers of the world to come, (aiōn )
inda Yesu, wanda ya sha gabanmu, ya shiga a madadinmu. Ya zama babban firist na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek. (aiōn )
into which the forerunner for us is entered, even Jesus, made after the order of Melchisedec an high-priest for ever. (aiōn )
Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
For the testimony is, Thou art a priest for ever after the order of Melchisedec. (aiōn )
shi wannan ya zama firist ta wurin rantsuwar da Allah ya yi da ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, ba kuwa zai canja zuciyarsa ba, ‘Kai firist ne na har abada.’” (aiōn )
(for they indeed were made priests without an oath; but he with an oath, by him who said unto him, “The Lord hath sworn, and will not repent, Thou art a priest for ever after the order of Melchisedec:”) (aiōn )
amma Yesu ba zai mutu ba, don haka zai zama firist har abada. (aiōn )
but this person, because he abideth for ever, hath a priesthood that passeth not over to another. (aiōn )
Gama doka takan naɗa babban firist a cikin mutane masu kāsawa; amma rantsuwar da ta zo bayan dokar, ta naɗa Ɗan, wanda aka mai da shi cikakke har abada. (aiōn )
For the law constitutes men high-priests, though they have infirmity; but the word of the oath, which is since the law, constitutes the Son, unto eternity completely perfect. (aiōn )
Bai shiga ta wurin jinin awaki da na maruƙa ba; amma ya shiga Wuri Mafi Tsarki sau ɗaya tak ta wurin jininsa, bayan ya samo madawwamiyar fansa. (aiōnios )
nor by the blood of goats and of calves, but by his own blood, he entered once for all into the holies, having obtained eternal redemption. (aiōnios )
balle jinin Kiristi, wanda ta wurin Ruhu madawwami ya miƙa kansa marar aibi ga Allah, ai, zai tsabtacce lamirinmu daga ayyukan da suke kai ga mutuwa, don mu bauta wa Allah mai rai! (aiōnios )
how much more shall the blood of Christ, who, by the eternal Spirit, offered up himself in sacrifice without blemish to God, cleanse our conscience from dead works, that we may perform divine service to the living God? (aiōnios )
Saboda haka Kiristi shi ne matsakancin sabon alkawari, don waɗanda aka kira su sami madawwamin gādon da aka yi alkawari, yanzu da ya mutu a matsayin mai fansa don yă’yantar da su daga zunuban da aka aikata a ƙarƙashin alkawari na farko. (aiōnios )
And for this cause he is the mediator of the new testament, that, death being suffered for the redemption of transgressions committed against the first testament, they who are called might receive the promise of an eternal inheritance. (aiōnios )
Da a ce haka ne, ai, da Kiristi ya sha wahala sau da yawa tun halittar duniya. Amma yanzu ya bayyana sau ɗaya tak a ƙarshen zamanai domin yă kawar da zunubi ta wurin miƙa kansa hadaya. (aiōn )
(for in that case he must have suffered often since the foundation of the world: ) but now once for all at the consummation of the ages hath he been manifested for the abolishing sin by the sacrifice of himself. (aiōn )
Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn )
By faith we understand that the worlds were exactly formed by the word of God, so that the visible objects were not made out of things which now appear. (aiōn )
Yesu Kiristi ba ya sākewa, shi ne a jiya, shi ne a yau, shi ne kuma har abada. (aiōn )
Jesus Christ is the same yesterday, to-day, and for ever. (aiōn )
Bari Allah na salama, wanda ta wurin jinin madawwamin alkawari ya tā da Ubangijinmu Yesu daga matattu, wannan Makiyayin tumaki mai girma, (aiōnios )
Now the God of peace, who brought again from the dead our Lord Jesus, the great pastor of the sheep, by the blood of the everlasting testament, (aiōnios )
yă kintsa ku da kowane abu mai kyau domin aikata nufinsa, bari kuma yă aikata abin da zai gamshe shi cikinmu, ta wurin Yesu Kiristi, a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn )
make you fit for every good work to do his will, producing in you that which is acceptable in his sight, through Jesus Christ; to whom be glory unto the everlasting ages. Amen. (aiōn )
Harshe ma wuta ne! A cikin duk gaɓoɓinmu, harshe shi ne tushen kowace irin mugunta, mai ɓata mutum gaba ɗaya, mai zuga zuciyar mutum ta tafasa, shi kuwa jahannama ce take zuga shi. (Geenna )
And the tongue is a fire, a world of iniquity: in such manner is the tongue placed among our members, that it defileth all the body, and setteth on fire the circle of nature; and is set on fire of hell. (Geenna )
Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn )
born again, not of corruptible seed, but of incorruptible, by the quickening word of God, and which abideth for ever. (aiōn )
amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn )
but the word of the Lord abideth for ever. And this is the word which by the gospel is preached unto you. (aiōn )
In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
If any man speak, let it be agreeably to the oracles of God; if any man act as a deacon, let it be from the strength which God supplieth: that in all things God may be glorified through Jesus Christ; to whom be glory and might for ever and ever. Amen. (aiōn )
Allah mai dukan alheri, wanda ya kira ku ga madawwamiyar ɗaukaka cikin Kiristi, bayan kun sha wahala na ɗan lokaci, shi da kansa zai raya ku, yă kuma sa ku yi ƙarfi, ku kahu, ku kuma tsaya daram. (aiōnios )
But the God of all grace, who hath called us to his eternal glory by Christ Jesus, when ye have suffered a little while, himself perfect, stablish, strengthen, settle you. (aiōnios )
Gare shi bari iko yă tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
To him be glory and might for ever and ever. Amen. (aiōn )
za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
but an entrance will thus be richly afforded you into the eternal kingdom of our Lord and Saviour Jesus Christ. (aiōnios )
Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
For if God spared not the angels when they sinned, but casting them bound in chains of darkness into hell, delivered them to be kept fast until the judgment; (Tartaroō )
Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn )
But grow in grace, and in the knowledge of our Lord and Saviour Jesus Christ. To him be glory now and unto the day of eternity. Amen. (aiōn )
Wannan Rai ya bayyana, muka kuwa gan shi, muka kuma shaida shi, muna kuwa yin muku shelar wannan rai madawwami, wanda dā yake tare da Uba, ya kuma bayyana a gare mu. (aiōnios )
(for the life was manifested, and we have beheld it, and bear testimony, and declare unto you that life eternal, which was with the Father, and was manifested to us; ) (aiōnios )
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
And the world is passing away, and the lust thereof, but he who doeth the will of God abideth for ever. (aiōn )
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
And this is the promise which he hath promised to us, even life eternal. (aiōnios )
Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
Every one who hateth his brother is a murderer; and ye know that no murderer hath life eternal abiding in him. (aiōnios )
Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
And this is the testimony, that God hath given life eternal to us; and this life is in his Son. (aiōnios )
Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
These things have I written to you who believe on the name of the Son of God, that ye may know that ye have life eternal, and that ye may believe on the name of the Son of God. (aiōnios )
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
But we know that the Son of God hath come, and hath given to us understanding, that we might know the true God; and we are in him that is true, in his Son Jesus the Messiah. HE is the true God, and the life eternal. (aiōnios )
Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn )
because of the truth which abideth in us, and shall be with us for ever: (aiōn )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
And the angels who preserved not their own primitive state, but deserted their proper abode, hath he reserved in everlasting chains under darkness, unto the judgment of the great day. (aïdios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
As Sodom and Gomorrha and the surrounding cities, in like manner with them abandoned to whoredom, and going after other flesh, are set forth an example, suffering the judicial punishment of eternal fire. (aiōnios )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
raging billows of the sea foaming out their own infamies; stars wandering from their courses, for whom the blackness of darkness for ever is reserved. (aiōn )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
preserve yourselves in the love of God, waiting for the mercy of our Lord Jesus Christ unto eternal life. (aiōnios )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )
to the only wise God our Saviour, be glory and majesty, might and dominion, both now and unto all eternity. Amen. (aiōn )
ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn )
and made us kings and priests to his God and Father; to him be glory and might for ever and ever. Amen. (aiōn )
Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn , Hadēs )
and I am the living one, though I was dead and lo! I am alive for evermore, Amen; and I hold the keys of hell and of death. (aiōn , Hadēs )
Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn )
And when these living beings give glory, and honour, and thanksgiving to him that sitteth on the throne, to him who liveth for ever and ever, (aiōn )
sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn )
the four and twenty presbyters prostrate themselves before him who is Seated on the throne, and worship him who liveth for ever and ever, and cast their crowns before the throne, saying, (aiōn )
Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn )
And every creature which is in heaven, and on the earth, and under the earth, and those who are on the sea, and all things which are therein, heard I, saying, To him who is seated on the throne, and to the lamb, be blessing, and honour, and glory, and might for ever and ever. (aiōn )
Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya. (Hadēs )
And I looked, and lo! a pale coloured horse, and one sat on it, whose name was Death, and the grave followed after him: and power was given to them to kill the fourth part of the earth with the sword, and with famine, and with death, and with the wild beasts of the earth. (Hadēs )
suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn )
saying, Amen: blessing, and glory, and wisdom, and thanksgiving, and honour, and power, and might be to our God for ever and ever. Amen. (aiōn )
Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos )
AND the fifth angel sounded, and I saw a star fall from heaven to the earth; and to him was given the key of the pit of the abyss of hell. (Abyssos )
Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos )
And he opened the pit of the abyss; and a smoke ascended out of the pit like the smoke of a vast furnace; and the sun and the air were darkened by the smoke of the pit. (Abyssos )
Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos )
And they had over them a king, the angel of the abyss of hell, whose name in Hebrew is Abaddon, and in Greek he is called Appollyon. (Abyssos )
Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn )
and he swore by him that liveth for ever and ever, who created the heaven and the things which are therein, and the earth and the things which are in it, and the sea, and the things which are therein, that time shall be no longer: (aiōn )
To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos )
And when they shall have finished their testimony, the beast which ascendeth out of hell shall make war with them, and shall overcome them, and put them to death. (Abyssos )
Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn )
And the seventh angel sounded; and there were great voices in heaven, saying, The kingdoms of the world are become our Lord’s, and his Messiah’s, and he shall reign for ever and ever. (aiōn )
Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios )
And I saw another angel flying in the midst of heaven, having the everlasting gospel to preach the glad tidings to the inhabitants of the earth, to every nation, and tribe, and tongue, and people, (aiōnios )
Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn )
and the smoke of their torment ascendeth for ever and ever: and they have no respite day nor night, who worship the beast and his image, and whosoever receiveth the brand of his name. (aiōn )
Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn )
And one of the four living beings gave unto the seven angels seven golden vases full of the wrath of God, who liveth for ever and ever. (aiōn )
Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos )
The beast which thou seest was, and is not; and shall come up out of the abyss of hell, and shall go into perdition: and the dwellers upon earth will wonder, (whose names are not written in the book of life from the foundation of the world, ) when they shall see the beast which was, and is not, though he is. (Abyssos )
Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn )
And the second time they said, Hallelujah. And her smoke ascended up for ever and ever. (aiōn )
Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr )
And the beast was seized upon, and with him the false prophet who performed the wonders before him, by which he deceived those who received the brand of the beast, and those who worshipped his image. They were both hurled alive into the lake of fire which burneth with brimstone. (Limnē Pyr )
Na kuma ga wani mala’ika yana saukowa daga sama, yana da mabuɗin Abis yana kuma riƙe da ƙaton sarƙa a hannunsa. (Abyssos )
AND I saw an angel descending from heaven, having the key of the abyss of hell, and a great chain in his hand: (Abyssos )
Ya jefa shi cikin Abis, ya kuma kulle ya sa hatimi a kansa, don a hana kada yă ƙara ruɗin al’ummai, sai shekarun nan dubu sun cika. Bayan wannan, dole a sake shi na ɗan lokaci. (Abyssos )
and cast him into the abyss, and shut him up, and put a seal upon it, that he might deceive the nations no more until the thousand years are completed: and after that he must be loosed a short time. (Abyssos )
Aka jefa Iblis da ya ruɗe su cikin tafkin farar wuta, inda aka jefa dabban nan da annabin ƙaryan nan. Za a ba su azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn , Limnē Pyr )
And the devil who deceived them was cast into the lake of fire and brimstone, where the beast and the false prophet are, and they shall be tormented day and night for ever and ever. (aiōn , Limnē Pyr )
Teku ya ba da matattu da suke cikinsa, mutuwa da Hades kuma suka ba da matattu da suke cikinsu, aka kuma yi wa kowane mutum shari’a bisa ga abin da ya aikata. (Hadēs )
And the sea gave up the dead that were in it, and death and the grave gave up the dead that were in them; and every one was judged according to his works. (Hadēs )
Sa’an nan aka jefar da mutuwa da kuma Hades cikin tafkin wuta. Tafkin wutar nan kuwa shi ne mutuwa ta biyu. (Hadēs , Limnē Pyr )
And death and the grave were cast into the lake of fire: this is the second death. (Hadēs , Limnē Pyr )
Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a cikin littafin rai ba, an jefar da shi cikin tafkin wutar nan. (Limnē Pyr )
And if any one was not found inscribed on the book of life, he was cast into the lake of fire. (Limnē Pyr )
Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.” (Limnē Pyr )
But to those who shrink back through fear, and to the infidels, and to the abominable, and to murderers, and to whoremongers, and to those who use magical incantations, and to idolaters, and to all liars, is their portion appointed in the lake which burneth with fire and brimstone; which is the second death. (Limnē Pyr )
Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
And there shall be no night there, and they have no need of a lamp, or the light of the sun; because the Lord God illumines them: and they shall reign for ever and ever. (aiōn )