< Ru’uya ta Yohanna 10 >

1 Sai na ga wani babban mala’ika yana saukowa daga sama. An lulluɓe shi da girgije, bakan gizo kuma yana kansa; fuskarsa tana kama da rana, ƙafafunsa kuma suna kama da ginshiƙan wuta.
AND I saw another mighty angel descending from heaven, clothed with a cloud; and a rainbow on his head, and his countenance as the sun, and his feet as pillars of fire:
2 Yana riƙe da ɗan ƙaramin naɗaɗɗen littafi, wanda yake a buɗe a hannunsa. Ya kafa ƙafarsa ta dama a kan teku ƙafarsa ta hagu kuma a kan ƙasa,
and he held in his hand a little book open; and he placed his right foot on the sea, and his left on the land,
3 ya kuma yi ihu da ƙarfi kamar rurin zaki. Da ya yi ihun, sai muryoyin tsawan nan bakwai suka yi magana.
and cried with a loud voice, as a lion roareth: and when he had cried, the seven thunders uttered their voices.
4 Sa’ad da tsawan nan bakwai kuwa suka yi magana, ina dab da rubutawa; amma na ji wata murya daga sama ta ce, “Rufe abin da tsawan nan bakwai suka faɗa kada ka rubuta.”
And when the seven thunders had uttered their voices, I was about to write: and I heard a voice from heaven saying to me, Seal up the things, which the seven thunders have spoken, and write them not down.
5 Sai mala’ikan da na gani na tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama.
And the angel which I saw standing upon the sea and upon the land lifted up his hand towards heaven,
6 Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn g165)
and he swore by him that liveth for ever and ever, who created the heaven and the things which are therein, and the earth and the things which are in it, and the sea, and the things which are therein, that time shall be no longer: (aiōn g165)
7 Amma a ranakun da mala’ika na bakwai na dab da busa ƙahonsa, za a cika asirin Allah, kamar yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
but that in the days of the blast of the seventh angel, when he shall sound, then shall the mystery of God be completed, as he spake by his own servants the prophets.
8 Sai muryar da na ji daga sama ta sāke magana da ni ta ce, “Tafi, ka karɓi naɗaɗɗen littafin da yake a buɗe a hannun mala’ikan da yake tsaye bisa teku da ƙasa.”
And the voice which I heard out of heaven again spoke to me, and said, Go take the little book which is open in the hand of the angel that standeth upon the sea and upon the land.
9 Sai na je wajen mala’ikan na ce masa yă ba ni ƙaramin naɗaɗɗen littafin. Ya ce mini, “Karɓa ka ci. Zai sa cikinka yă yi tsami, amma ‘a bakinka zai zama da zaƙi kamar zuma.’”
And I went up to the angel, saying unto him, Give me that little book. And he saith to me, Take it, and eat it up; and it will make thy belly bitter, though in thy mouth it will be sweet as honey.
10 Na karɓi ƙaramin naɗaɗɗen littafin daga hannun mala’ikan na kuma ci. Ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma sa’ad da na cinye, cikina ya yi tsami.
And I took the little book out of the angel’s hand, and ate it up; and it was in my mouth as honey sweet; yet when I had eaten it, my belly was made bitter.
11 Sa’an nan aka ce mini, “Dole ne ka sāke yin annabci game da mutane masu yawa, al’ummai, harsuna da kuma sarakuna.”
And he said to me, Thou must prophesy again before many people, and nations, and tongues, and monarchs.

< Ru’uya ta Yohanna 10 >