< 2 Bitrus 2 >

1 Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
BUT there were false prophets among the people, as there will be false teachers also among you, who wickedly introduce damnable heresies, and deny the sovereign Lord who bought them, bringing on themselves swift destruction.
2 Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
And many will go out of the way after their fatal errors; by means of whom the way of truth will be injuriously reviled.
3 Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
And with plausible speeches will they avariciously make gain of you whose condemnation from of old lingereth not, and their perdition doth not slumber.
4 Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō g5020)
For if God spared not the angels when they sinned, but casting them bound in chains of darkness into hell, delivered them to be kept fast until the judgment; (Tartaroō g5020)
5 in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
and spared not the old world, but guarded safely Noah the eighth person, the preacher of righteousness, when he brought a deluge on the world of the ungodly:
6 in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
and reducing the cities of Sodom and Gomorrah to ashes, condemned them to final destruction, making them an example for all who in future should live ungodly;
7 in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
but righteous Lot, afflicted grievously with the infamously impure conduct of those lawless men, he plucked out:
8 (adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
for by seeing and hearing, that righteous man whilst sojourning among them, suffered torment day by day in his righteous soul from their lawless doings;
9 in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
the Lord knoweth how to deliver the godly out of temptation, but to reserve the wicked unto the day of judgment to be punished:
10 Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
especially such as walk after the flesh in the eager pursuit of defilement, and despise government. Daring, self-sufficient, they tremble not at dignities, railing against them.
11 duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
Whereas the angels, though so much greater in might and power, bring not a reviling accusation against them before the Lord.
12 Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
But these men, as the naturally irrational brute beasts, made to be taken and destroyed, speaking evil of the things of which they are ignorant, will perish by their own corruption;
13 Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
receiving the recompence of iniquity, counting daily luxury their pleasure; spots and blemishes, when they feast together with you; riotously indulging in their own delusions:
14 Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
having eyes full of adultery, and insatiable of sin; ensnaring souls of no stability; having a heart practised in all the wiles of covetousness; children for a curse:
15 Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
who forsaking the strait road are gone out of the way, following the path of Balaam the son of Bosor who loved the wages of iniquity.
16 Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
But received a reproof for his peculiar transgression: the dumb ass articulating with a human voice restrained the perverseness of the prophet.
17 Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
These are fountains without water, clouds driven by a hurricane; for whom the blackness of darkness for ever is reserved. (questioned)
18 Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
Uttering pompous discourses of inanity, ensnaring by the lusts of the flesh, by lascivious impurities, those who had truly escaped from such as live in a course of delusion.
19 Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
Preaching liberty to them, while they themselves are the slaves of corruption: for by whatever a man is overcome, by that also he is enslaved.
20 In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
For if having escaped from the defilements of the world by the knowledge of our Lord and Saviour Jesus Christ, they are again enveloped by them and overcome, their last deeds are worse than the first.
21 Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
For it had been better for them never to have been acquainted with the way of righteousness, than, after knowing it, to have turned aside from the holy commandment delivered unto them.
22 A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”
But the true proverb is verified in them, The dog hath returned to his own vomit; and the sow which was washed to its wallowing in the mire.

< 2 Bitrus 2 >