< Romawa 11 >
1 To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
I SAY then, Hath God rejected his people? God forbid. For I also am an Israelite, of the seed of Abraham, of the tribe of Benjamin.
2 Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
God hath not rejected his people whom he foreknew. Know ye not what the scripture saith of Elias? how he maketh intercession with God against Israel, saying,
3 “Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
“Lord, they have killed thy prophets, and digged down thine altars; and I only am left, and they seek my life.”
4 Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
But what saith the oracle of God to him? “I have left to myself seven thousand men who have not bowed the knee to Baal.”
5 Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
So then at this present time also there is a remnant according to the election of grace.
6 In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
But if by grace, it is no more by works: otherwise grace is no more grace. But if by works, it is no more grace: otherwise work is no more work.
7 To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
What then is the result? Israel hath not obtained that which it seeketh; but the election hath obtained it, and the rest were blinded,
8 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
as it is written, “God hath given them the spirit of slumber, eyes that they should not see, and ears that they should not hear; unto this present day.”
9 Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
And David saith, “Let their table be for a snare, and for a trap, and for a stumbling-block, and for a recompence unto them:
10 Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
let their eyes be blinded, that they may not see, and bow down their back continually.”
11 Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
I say then, Have they stumbled so as to fall? God forbid: but by their stumbling salvation is come to the Gentiles, to provoke them to jealousy.
12 Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
For if their stumbling is the riches of the world, and their diminution the riches of the Gentiles; how much more their fulness?
13 Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
For I address myself to you Gentiles; inasmuch as I am indeed the apostle of the Gentiles, I exalt my ministry:
14 da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
if by any means I might provoke to jealousy my flesh, and save some of them.
15 Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
For if the rejection of them is the reconciliation of the world, what shall their recovery be, but life from the dead?
16 In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
Now if the first fruits be holy, so is the mass: and if the root be holy, so are the branches.
17 In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
But if some of the branches have been broken off, and thou though a wild olive hast been grafted in among them, and become a partaker of the root and fatness of the olive tree;
18 kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
boast not against the branches. But if thou boast, thou bearest not the root, but the root thee.
19 To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
Wilt thou say then, The branches were broken off, that I might be grafted in?
20 Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
Admitted; by unbelief they were broken off, and thou standest by faith. Be not high minded, but fear:
21 Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
for if God spared not the native branches, tremble lest he spare not thee.
22 Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
Behold therefore the kindness and severity of God: to those indeed who fell, severity; but unto thee, kindness, if thou continuest in that kindness: otherwise thou also shalt be cut off.
23 In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
But they also, if they continue not in unbelief, shall be grafted in: for God is able to graft them in again.
24 Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
For if thou hast been cut out of the naturally wild olive, and contrary to nature hast been grafted into the good olive: how much more shall these, which are native branches, be grafted into their own olive tree?
25 Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
For I would not that you should be ignorant, brethren, of this mystery, lest ye should be wise in your own conceits; that blindness in part is come on Israel, until the fulness of the Gentiles be come in.
26 Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
And so all Israel shall be saved: as it is written, “The Deliverer shall go forth out of Sion, and shalt turn away ungodliness from Jacob;
27 Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
and this is my covenant with them, When I shall take away their sins.”
28 Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
As concerning the gospel indeed, they are now enemies for your sakes: as concerning the election, they are beloved for the fathers’ sake.
29 gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
For unchangeable are the gifts and the calling of God.
30 Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
For as ye also in times past did not believe in God, but now have obtained mercy through their unbelief:
31 haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
so also these now have not believed in your mercy, that they also might obtain mercy.
32 Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē )
For God hath shut up all in unbelief, that he might have mercy upon all. (eleēsē )
33 Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
O the depth of the riches both of the wisdom and knowledge of God! how unsearchable are his judgments, and how incomprehensible his ways!
34 “Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
For who hath known the mind of the Lord, or who hath been admitted his counsellor?
35 “Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
Or who hath first given unto him, and it shall be repaid him again?
36 Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn )
Because by him, and through him, and for him, are all things, to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )