< Zabura 36 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
The transgression of the wicked man says within my heart, There is no fear of God before his eyes.
2 Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
For he flatters himself in his own eyes, that his iniquity will not be found out and be hated.
3 Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
The words of his mouth are iniquity and deceit. He has ceased to be wise and to do good.
4 Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
He devises iniquity upon his bed. He sets himself in a way that is not good. He does not abhor evil.
5 Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
Thy loving kindness, O Jehovah, is in the heavens, thy faithfulness to the skies.
6 Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
Thy righteousness is like the mountains of God. Thy judgments are a great deep. O Jehovah, thou preserve man and beast.
7 Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
How precious is thy loving kindness, O God, and the sons of men take refuge under the shadow of thy wings.
8 Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
They shall be abundantly satisfied with the fatness of thy house, and thou will make them drink of the river of thy pleasures.
9 Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
For with thee is the fountain of life. In thy light we shall see light.
10 Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
O continue thy loving kindness to those who know thee, and thy righteousness to the upright in heart.
11 Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
Let not the foot of pride come against me, and let not the hand of sinners drive me away.
12 Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!
There are the workers of iniquity fallen. They are thrust down, and shall not be able to rise.