< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
in finem pro adsumptione matutina psalmus David Deus Deus meus respice me quare me dereliquisti longe a salute mea verba delictorum meorum
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Deus meus clamabo per diem et non exaudies et nocte et non ad insipientiam mihi
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
tu autem in sancto habitas Laus Israhel
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
in te speraverunt patres nostri speraverunt et liberasti eos
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
ad te clamaverunt et salvi facti sunt in te speraverunt et non sunt confusi
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
ego autem sum vermis et non homo obprobrium hominum et abiectio plebis
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
omnes videntes me deriserunt me locuti sunt labiis moverunt caput
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
speravit in Domino eripiat eum salvum faciat eum quoniam vult eum
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
quoniam tu es qui extraxisti me de ventre spes mea ab uberibus matris meae
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
in te proiectus sum ex utero de ventre matris meae Deus meus es tu
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
ne discesseris a me quoniam tribulatio proxima est quoniam non est qui adiuvet
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
circumdederunt me vituli multi tauri pingues obsederunt me
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
aperuerunt super me os suum sicut leo rapiens et rugiens
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
sicut aqua effusus sum et dispersa sunt universa ossa mea factum est cor meum tamquam cera liquescens in medio ventris mei
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
aruit tamquam testa virtus mea et lingua mea adhesit faucibus meis et in limum mortis deduxisti me
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
quoniam circumdederunt me canes multi concilium malignantium obsedit me foderunt manus meas et pedes meos
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
dinumeraverunt omnia ossa mea ipsi vero consideraverunt et inspexerunt me
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
diviserunt sibi vestimenta mea et super vestem meam miserunt sortem
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
tu autem Domine ne elongaveris auxilium tuum ad defensionem meam conspice
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
erue a framea animam meam et de manu canis unicam meam
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
salva me ex ore leonis et a cornibus unicornium humilitatem meam
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
narrabo nomen tuum fratribus meis in media ecclesia laudabo te
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
qui timetis Dominum laudate eum universum semen Iacob magnificate eum
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
timeat eum omne semen Israhel quoniam non sprevit neque dispexit deprecationem pauperis nec avertit faciem suam a me et cum clamarem ad eum exaudivit me
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
apud te laus mea in ecclesia magna vota mea reddam in conspectu timentium eum
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
edent pauperes et saturabuntur et laudabunt Dominum qui requirunt eum vivent corda eorum in saeculum saeculi
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
reminiscentur et convertentur ad Dominum universi fines terrae et adorabunt in conspectu eius universae familiae gentium
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
quoniam Dei est regnum et ipse dominabitur gentium
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
manducaverunt et adoraverunt omnes pingues terrae in conspectu eius cadent omnes qui descendunt in terram
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
et anima mea illi vivet et semen meum serviet ipsi
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
adnuntiabitur Domino generatio ventura et adnuntiabunt iustitiam eius populo qui nascetur quem fecit Dominus

< Zabura 22 >