< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
parabolae Salomonis filii David regis Israhel
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
ad sciendam sapientiam et disciplinam
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
ad intellegenda verba prudentiae et suscipiendam eruditionem doctrinae iustitiam et iudicium et aequitatem
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
ut detur parvulis astutia adulescenti scientia et intellectus
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
audiens sapiens sapientior erit et intellegens gubernacula possidebit
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
animadvertet parabolam et interpretationem verba sapientium et enigmata eorum
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
timor Domini principium scientiae sapientiam atque doctrinam stulti despiciunt
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
audi fili mi disciplinam patris tui et ne dimittas legem matris tuae
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
ut addatur gratia capiti tuo et torques collo tuo
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
fili mi si te lactaverint peccatores ne adquiescas
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
si dixerint veni nobiscum insidiemur sanguini abscondamus tendiculas contra insontem frustra
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
degluttiamus eum sicut infernus viventem et integrum quasi descendentem in lacum (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
omnem pretiosam substantiam repperiemus implebimus domos nostras spoliis
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
sortem mitte nobiscum marsuppium unum sit omnium nostrum
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
fili mi ne ambules cum eis prohibe pedem tuum a semitis eorum
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
pedes enim illorum ad malum currunt et festinant ut effundant sanguinem
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
frustra autem iacitur rete ante oculos pinnatorum
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
ipsique contra sanguinem suum insidiantur et moliuntur fraudes contra animas suas
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
sic semitae omnis avari animas possidentium rapiunt
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
sapientia foris praedicat in plateis dat vocem suam
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
in capite turbarum clamitat in foribus portarum urbis profert verba sua dicens
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
usquequo parvuli diligitis infantiam et stulti ea quae sibi sunt noxia cupiunt et inprudentes odibunt scientiam
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
convertimini ad correptionem meam en proferam vobis spiritum meum et ostendam verba mea
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
quia vocavi et rennuistis extendi manum meam et non fuit qui aspiceret
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
despexistis omne consilium meum et increpationes meas neglexistis
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
ego quoque in interitu vestro ridebo et subsannabo cum vobis quod timebatis advenerit
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
cum inruerit repentina calamitas et interitus quasi tempestas ingruerit quando venerit super vos tribulatio et angustia
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
tunc invocabunt me et non exaudiam mane consurgent et non invenient me
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
eo quod exosam habuerint disciplinam et timorem Domini non susceperint
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
nec adquieverint consilio meo et detraxerint universae correptioni meae
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
comedent igitur fructus viae suae suisque consiliis saturabuntur
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
aversio parvulorum interficiet eos et prosperitas stultorum perdet illos
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
qui autem me audierit absque terrore requiescet et abundantia perfruetur malorum timore sublato

< Karin Magana 1 >