< Zabura 137 >
1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
De David. Sur les fleuves de Babylone nous nous sommes assis, et nous avons pleuré, en nous souvenant de Sion.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
Nous avons suspendu nos harpes aux saules, qui sont au milieu de la contrée.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
Car ceux qui nous avaient faits captifs nous demandaient les paroles de nos cantiques; et ceux qui nous avaient emmenés nous disaient: Chantez-nous un hymne des cantiques de Sion!
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Comment chanterons-nous un cantique du Seigneur sur une terre étrangère?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
Si je t'oublie, Jérusalem, que ma main droite s'oublie elle-même!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Si je ne me propose Jérusalem comme le principe de mes joies; si je ne me souviens point de toi, que ma langue s'attache à mon gosier.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Souviens-toi, Seigneur, des fils d'Édom, qui, au dernier jour de Jérusalem, disaient; Détruisez-la, détruisez-la jusqu'en ses fondements!
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
Fille de Babylone, infortunée! heureux celui qui te rendra le mal en retour du mal que tu as fait!
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
Heureux celui qui saisira tes petits enfants et les écrasera contre la pierre!