< Zabura 138 >

1 Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
De David. Seigneur, je te rendrai gloire de toute mon âme, et je te chanterai mes psaumes devant les anges, parce que tu as écouté les paroles de ma bouche.
2 Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
Je t'adorerai en ton saint temple, et je rendrai gloire à ton nom, à cause de ta miséricorde et de ta vérité; car tu as exalté ton saint nom au- dessus de toutes choses.
3 Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
En quelque jour que je t'invoque, aussitôt exauce-moi; et tu agrandiras mon âme par ta force.
4 Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
Seigneur, que tous les rois de la terre te rendent gloire; car ils ont ouï toutes les paroles de ta bouche.
5 Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
Et qu'ils chantent dans les voies du Seigneur; car la gloire du Seigneur est grande.
6 Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
Car le Seigneur, quoique très élevé, regarde les humbles, et reconnaît de loin les superbes.
7 Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
Si je marche au milieu des tribulations, tu me vivifieras; tu as étendu les mains contre la fureur de mes ennemis, et ta droite m'a sauvé.
8 Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.
Le Seigneur les rétribuera en ma faveur; Seigneur, ta miséricorde est éternelle: ne méprise pas l'œuvre de tes mains.

< Zabura 138 >