< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Cántico gradual: de David. YO me alegré con los que me decían: A la casa de Jehová iremos.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Nuestros pies estuvieron en tus puertas, oh Jerusalem;
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, que se ha edificado como una ciudad que está bien unida entre sí.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Y allá subieron las tribus, las tribus de JAH, [conforme] al testimonio [dado] á Israel, para alabar el nombre de Jehová.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Porque allá están las sillas del juicio, las sillas de la casa de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pedid la paz de Jerusalem: sean prosperados los que te aman.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Haya paz en tu antemuro, [y] descanso en tus palacios.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Por amor de mis hermanos y mis compañeros hablaré ahora paz de ti.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
A causa de la casa de Jehová nuestro Dios, buscaré bien para ti.