< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
LOS proverbios de Salomón, hijo de David, rey de Israel:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Para entender sabiduría y doctrina; para conocer las razones prudentes;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Para recibir el consejo de prudencia, justicia, y juicio y equidad;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Para dar sagacidad á los simples, y á los jóvenes inteligencia y cordura.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Oirá el sabio, y aumentará el saber; y el entendido adquirirá consejo;
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Para entender parábola y declaración; palabras de sabios, y sus dichos oscuros.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
El principio de la sabiduría es el temor de Jehová: los insensatos desprecian la sabiduría y la enseñanza.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Oye, hijo mío, la doctrina de tu padre, y no desprecies la dirección de tu madre:
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Porque adorno de gracia serán á tu cabeza, y collares á tu cuello.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Hijo mío, si los pecadores te quisieren engañar, no consientas.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Si dijeren: Ven con nosotros, pongamos asechanzas á la sangre, acechemos sin motivo al inocente;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Los tragaremos vivos como el sepulcro, y enteros, como los que caen en sima; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Hallaremos riquezas de todas suertes, henchiremos nuestras casas de despojos;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Echa tu suerte entre nosotros; tengamos todos una bolsa:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Hijo mío, no andes en camino con ellos; aparta tu pie de sus veredas:
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Porque sus pies correrán al mal, é irán presurosos á derramar sangre.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Porque en vano se tenderá la red ante los ojos de toda ave;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Mas ellos á su propia sangre ponen asechanzas, y á sus almas tienden lazo.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Tales son las sendas de todo el que es dado á la codicia, [la cual] prenderá el alma de sus poseedores.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
La sabiduría clama de fuera, da su voz en las plazas:
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
Clama en los principales lugares de concurso; en las entradas de las puertas de la ciudad dice sus razones:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
¿Hasta cuándo, oh simples, amaréis la simpleza, y los burladores desearán el burlar, y los insensatos aborrecerán la ciencia?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Volveos á mi reprensión: he aquí yo os derramaré mi espíritu, y os haré saber mis palabras.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Por cuanto llamé, y no quisisteis; extendí mi mano, y no hubo quien escuchase;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Antes desechasteis todo consejo mío, y mi reprensión no quisisteis:
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
También yo me reiré en vuestra calamidad, y me burlaré cuando [os] viniere lo que teméis;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Cuando viniere como una destrucción lo que teméis, y vuestra calamidad llegare como un torbellino; cuando sobre vosotros viniere tribulación y angustia.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Entonces me llamarán, y no responderé; buscarme han de mañana, y no me hallarán:
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Por cuanto aborrecieron la sabiduría, y no escogieron el temor de Jehová,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Ni quisieron mi consejo, y menospreciaron toda reprensión mía:
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Comerán pues del fruto de su camino, y se hartarán de sus consejos.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Porque el reposo de los ignorantes los matará, y la prosperidad de los necios los echará á perder.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Mas el que me oyere, habitará confiadamente, y vivirá reposado, sin temor de mal.

< Karin Magana 1 >