< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Spreuken van Salomon, den zoon van David, Den koning van Israël:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Ze leren u kennen wijsheid en tucht, Ze geven u begrip voor verstandige woorden;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Ze voeden u op tot heilzame tucht, Rechtschapenheid, plichtsbesef en oprechtheid.
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Aan de onnozelen schenken ze ervaring, Aan jonge mensen doordachte kennis.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Als een wijze ze hoort, zal hij zijn inzicht verdiepen, Een verstandig mens zal er ideeën door krijgen;
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Spreuk en strikvraag zal hij doorzien, De woorden der wijzen en hun problemen.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Het ontzag voor Jahweh is de grondslag der wijsheid; Maar ongelovigen lachen om wijsheid en tucht.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Mijn zoon, luister dus naar de wenken van uw vader, Sla niet in de wind, wat uw moeder u leerde;
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Want het siert uw hoofd als een krans, Uw hals als een snoer.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Mijn zoon, als zondaars u willen verleiden, stem niet toe,
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Als ze u zeggen: Ga met ons mee, Laat ons loeren op bloed, Laat ons zo maar onschuldigen belagen,
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Gelijk de onderwereld hen levend verslinden, Als zij, die ten grave dalen, geheel en al; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Allerlei kostbare schatten zullen we vinden, Onze huizen vullen met buit;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Ge moogt meeloten in onze kring, Eén buidel zullen we samen delen!
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Mijn zoon, ga dan niet met hen mee, En houd uw voet af van hun pad;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Want hun voeten ijlen naar het kwade, En haasten zich, om bloed te vergieten.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Maar zoals het niet geeft, of het net wordt gespannen, Terwijl alle vogels het zien:
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Zo loeren ze slechts op hun eigen bloed, En belagen ze hun eigen leven!
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Zo gaat het allen, die uit zijn op oneerlijke winst: Deze beneemt zijn bezitters het leven.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
De wijsheid roept luid in de straten, Op de pleinen verheft ze haar stem;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
Ze roept op de tinne der muren, En spreekt aan de ingang der poorten:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Hoe lang nog, dommen, blijft gij liever onnozel, Blijven de eigenwijzen verwaand, Willen de dwazen van geen wijsheid horen?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Keert u tot mijn vermaning; Dan stort ik mijn geest over u uit, En maak u mijn woorden bekend.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Maar zo ge weigert, als ik roep, En niemand er op let, als ik mijn hand verhef;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Zo ge mijn raad geheel en al in de wind slaat, En van mijn vermaning niet wilt weten:
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Zal ik lachen, wanneer het u slecht gaat, Zal ik spotten, wanneer uw verschrikking komt als een onweer;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Wanneer uw ongeluk nadert als een orkaan, Wanneer benauwdheid en angst u overvallen!
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Dan zal men mij roepen, maar zal ik niet antwoorden, Zal men mij zoeken, maar mij niet vinden!
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Omdat ze van wijsheid niets wilden weten, En het ontzag voor Jahweh niet hebben verkozen,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Van mijn raad niets moesten hebben, En al mijn vermaan in de wind hebben geslagen:
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Zullen ze eten de vrucht van hun wandel, Verzadigd worden met wat ze beraamden.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Want de onnozelen komen door hun onverschilligheid om, De dwazen storten door hun lichtzinnigheid in het verderf;
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Maar die naar mij luistert, zal in veiligheid wonen, Bevrijd van de vrees voor de rampen!

< Karin Magana 1 >