< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Ndipo Elihu akasema:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“Je, unadhani hili ni haki? Wewe unasema, ‘Nina haki mbele za Mungu.’
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Bado unamuuliza, ‘Ni faida gani nimepata, na imenifaidi nini kwa kutokutenda dhambi?’
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
“Ningependa nikujibu wewe pamoja na marafiki zako walio pamoja nawe.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Tazama juu mbinguni ukaone; yaangalie mawingu yaliyo juu sana juu yako.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Je, ukitenda dhambi, inamdhuruje Mungu? Kama dhambi zako zikiwa nyingi, hilo linamfanyia nini Mungu?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Kama wewe ni mwadilifu, unampa nini, au yeye anapokea nini mkononi kwako?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Uovu wako unamdhuru tu mtu mwingine kama wewe, nayo haki yako inawafaa wanadamu tu.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
“Wanadamu hulia kwa kulemewa na mateso; huomba msaada kutoka mkono wenye nguvu.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Lakini hakuna asemaye, ‘Yuko wapi Mungu Muumba wangu, yeye anifanyaye niimbe usiku,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
yeye atufundishaye sisi zaidi kuliko wanyama wa dunia, na kutufanya wenye hekima kuliko ndege wa angani?’
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Yeye hajibu wakati watu waliapo kwa sababu ya kiburi cha watu waovu.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Naam, Mungu hasikilizi maombi yao ya ubatili; Mwenyezi hayazingatii.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Si zaidi sana kwamba hatakusikiliza wewe usemapo humwoni, tena ya kwamba shauri lako liko mbele zake na wewe lazima umngojee,
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
pia zaidi, kwamba hasira yake kamwe haiadhibu wala haangalii uovu hata kidogo?
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Hivyo Ayubu hufumbua kinywa chake kwa maneno yasiyo na maana; anaongea maneno mengi bila maarifa.”

< Ayuba 35 >