< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu akaendelea kusema:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
“Nivumilie kidogo zaidi nami nitakuonyesha kwamba yako mengi zaidi ya kusemwa kwa ajili ya Mungu.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Ninayapata maarifa yangu kutoka mbali, nami nitamhesabia haki Muumba wangu.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Uwe na hakika kwamba maneno yangu si ya uongo; mmoja aliye mkamilifu katika maarifa yuko pamoja na wewe.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
“Mungu ni mwenye nguvu, lakini hamdharau mwanadamu; ni mwenye nguvu, naye ni thabiti katika shauri lake.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Hawaachi waovu waendelee kuishi, bali huwapa walioteswa haki yao.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Yeye haondoi macho yake kwa wenye haki; huwaketisha penye viti vya enzi pamoja na wafalme na kuwatukuza milele.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Lakini ikiwa watu wamefungwa kwenye minyororo, wakiwa wameshikiliwa na kamba za mateso,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
huwaonyesha yale waliyoyatenda, kwamba wametenda dhambi kwa majivuno.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Huwafanya wao kusikia maonyo, na huwaagiza kutubu uovu wao.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Kama wakitii na kumtumikia, wataishi siku zao zilizobaki katika mafanikio, na miaka yao katika utoshelevu.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Lakini wasiposikiliza, wataangamia kwa upanga, nao watakufa pasipo maarifa.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
“Wasiomcha Mungu moyoni mwao huficha chuki; hata anapowafunga, hawamwombi msaada.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Wanakufa wangali vijana, miongoni mwa wanaume hanithi wa mahali pa kuabudia miungu.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Bali wao wanaoteseka huwaokoa katika mateso yao, na kuzungumza nao katika dhiki zao.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
“Yeye anakubembeleza utoke katika mataya ya dhiki, ili kukuweka mahali palipo na nafasi mbali na kizuizi, hadi kwenye meza yako ya faraja iliyojaa vyakula vizuri.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Lakini sasa umelemewa na hukumu kwa ajili ya uovu; hukumu na haki vimekukamata.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Uwe mwangalifu ili yeyote asikushawishi kwa utajiri; usipotoshwe kwa fungu kubwa la rushwa.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Je, utajiri wako hata nguvu zako nyingi vinaweza kukusaidia usiingie kwenye dhiki?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Usiutamani usiku uje, ili uwaburute watu mbali na nyumba zao.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Jihadhari usigeukie uovu, ambao unaupenda zaidi kuliko mateso.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
“Mungu ametukuzwa katika nguvu zake. Ni nani aliye mwalimu kama yeye?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Ni nani aliyemwelekeza katika njia zake, au kumwambia, ‘Wewe umetenda yasiyo sawa’?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Kumbuka kuzitukuza kazi zake, ambazo watu wamezisifu katika wimbo.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Wanadamu wote wameiona; watu wanaikazia macho kwa mbali.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Tazama jinsi Mungu alivyo mkuu, kupita ufahamu wetu! Hesabu ya miaka yake haitafutiki.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
“Yeye huvuta juu matone ya maji, ayachujayo kama mvua kutoka kwenye vijito;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
mawingu huangusha chini maji yake, nayo mvua nyingi huwanyeshea wanadamu.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Ni nani ajuaye jinsi ayatandazavyo mawingu, jinsi angurumavyo kutoka hemani mwake.
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Tazama jinsi anavyotandaza umeme wa radi kumzunguka, naye huvifunika vilindi vya bahari.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Hivi ndivyo atawalavyo mataifa, na kuwapa chakula kwa wingi.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Huujaza mkono wake kwa umeme wa radi, na kuuagiza kulenga shabaha yake.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Ngurumo zake hutangaza dhoruba inayokuja; hata mifugo hujulisha kukaribia kwake.

< Ayuba 36 >