< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Elihu spake moreouer, and said,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Thinkest thou this right, that thou hast said, I am more righteous then God?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
For thou hast said, What profiteth it thee and what auaileth it me, to purge me from my sinne?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Therefore will I answere thee, and thy companions with thee.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Looke vnto the heauen, and see and behold the cloudes which are hyer then thou.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If thou sinnest, what doest thou against him, yea, when thy sinnes be many, what doest thou vnto him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If thou be righteous, what giuest thou vnto him? or what receiueth he at thine hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Thy wickednesse may hurt a man as thou art: and thy righteousnes may profite ye sonne of man.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
They cause many that are oppressed, to crye, which crye out for ye violence of the mightie.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But none saieth, Where is God that made me, which giueth songs in the nyght?
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Which teacheth vs more then the beastes of the earth, and giueth vs more wisdome then the foules of the heauen.
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Then they crye because of the violence of the wicked, but he answereth not.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Surely God will not heare vanitie, neyther will the Almightie regard it.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Although thou sayest to God, Thou wilt not regard it, yet iudgement is before him: trust thou in him.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
But nowe because his anger hath not visited, nor called to count the euill with great extremitie,
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Therfore Iob openeth his mouth in vaine, and multiplieth wordes without knowledge.

< Ayuba 35 >