< Ayuba 36 >
Elihu also proceeded and sayde,
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Suffer me a litle, and I will instruct thee: for I haue yet to speake on Gods behalfe.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will fetche my knowledge afarre off, and will attribute righteousnes vnto my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For truely my wordes shall not be false, and he that is perfect in knowledge, speaketh with thee.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Behold, the mighty God casteth away none that is mighty and valiant of courage.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He mainteineth not the wicked, but he giueth iudgement to the afflicted.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He withdraweth not his eyes from the righteous, but they are with Kings in ye throne, where he placeth them for euer: thus they are exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
And if they bee bound in fetters and tyed with the cordes of affliction,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Then will he shewe them their worke and their sinnes, because they haue bene proude.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He openeth also their eare to discipline, and commandeth them that they returne from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they obey and serue him, they shall end their dayes in prosperity, and their yeres in pleasures.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they wil not obey, they shall passe by the sworde, and perish without knowledge.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
But the hypocrites of heart increase the wrath: for they call not when he bindeth them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Their soule dyeth in youth, and their life among the whoremongers.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
He deliuereth the poore in his affliction, and openeth their eare in trouble.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Euen so woulde he haue taken thee out of the streight place into a broade place and not shut vp beneath: and that which resteth vpon thy table, had bene full of fat.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But thou art ful of the iudgement of the wicked, though iudgement and equitie maintaine all things.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
For Gods wrath is, least hee should take that away in thine abundance: for no multitude of giftes can deliuer thee.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Wil he regard thy riches? he regardeth not golde, nor all them that excel in strength.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Be not carefull in the night, howe he destroyeth the people out of their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Take thou heede: looke not to iniquitie: for thou hast chosen it rather then affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Beholde, God exalteth by his power: what teacher is like him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who hath appointed to him his way? or who can say, Thou hast done wickedly?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Remember that thou magnifie his worke, which men behold.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
All men see it, and men beholde it afarre off.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Beholde, God is excellent, and we knowe him not, neither can the nomber of his yeres bee searched out.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
When he restraineth the droppes of water, the rayne powreth down by the vapour thereof,
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Which raine the cloudes do droppe and let fall abundantly vpon man.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Who can know the diuisions of ye clouds and the thunders of his tabernacle?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Beholde, he spreadeth his light vpon it, and couereth the bottome of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
For thereby hee iudgeth the people, and giueth meate abundantly.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
He couereth the light with the clouds, and commandeth them to go against it.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
His companion sheweth him thereof, and there is anger in rising vp.