< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Then Job answered and said,
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
“Even today my complaint is bitter; my hand is heavy because of my groaning.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Oh, that I knew where I might find him! Oh, that I might come to his place!
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
I would lay my case in order before him and fill my mouth with arguments.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
I would learn the words with which he would answer me and would understand what he would say to me.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Would he argue against me in the greatness of his power? No, he would pay attention to me.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
There the upright person might argue with him. In this way I would be acquitted forever by my judge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
See, I go eastward, but he is not there, and westward, but I cannot perceive him.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
To the north, where he is at work, but I cannot see him, and to the south, where he hides himself so that I cannot see him.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
But he knows the way that I take; when he has tested me, I will come out like gold.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
My foot has held fast to his steps; I have kept to his way and turned not aside.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
I have not gone back from the commandment of his lips; I have treasured the words of his mouth more than my portion of food.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
But he is one of a kind, who can turn him back? What he desires, he does.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
For he carries out his decree against me; there are many like them.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Therefore, I am terrified in his presence; when I think about him, I am afraid of him.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
For God has made my heart weak; the Almighty has terrified me.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
I have not been brought to an end by darkness, because of the thick darkness that covers the gloom of my face.