< Ayuba 24 >

1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
Why are times for judging wicked people not set by the Almighty? Why do not those who are faithful to God see his days of judgment come?
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
There are wicked people who remove boundary markers; there are wicked people who take away flocks by force and put them in their own pastures.
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
They drive away the donkey of those without fathers; they take the widow's ox as security.
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
They force needy people out of their path; poor people of the earth all hide themselves from them.
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
See, these poor people go out to their work like wild donkeys in the wilderness, looking carefully for food; perhaps the Arabah will provide them food for their children.
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
Poor people reap in the night in other people's fields; they glean grapes from the harvest of those wicked people.
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
They lie naked all night without clothing; they have no covering in the cold.
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
They are wet with the showers of the mountains; they lie next to large rocks because they have no shelter.
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
There are wicked people who pluck orphans from their mothers' breast, and wicked people who take children as security from poor people.
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
But the poor people go about naked without clothing; although they go hungry, they carry bundles of grain belonging to other people.
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
The poor people make oil within the walls of those wicked men; they tread the wicked men's winepresses, but they themselves suffer thirst.
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
From out of the city the dying groan, and the throat of the wounded cries out for help. But God does not ascribe blame
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
Some of these wicked people rebel against the light; they know not its ways, nor do they stay in its paths.
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
Before daylight the murderer rises and he kills poor and needy people; in the night he is like a thief.
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
Also, the eye of the adulterer waits for the twilight; he says, 'No eye will see me.' He disguises his face.
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
In the darkness wicked people dig into houses; but they shut themselves up in the daytime; they do not care for the light.
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
For all of them, thick darkness is like the morning; for they are friends with the terrors of thick darkness.
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
Swiftly they pass away, however, like foam on the surface of the waters; their portion of the land is cursed; no one goes to work in their vineyards.
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
As drought and heat melt away the snow into waters, so Sheol takes away those who have sinned. (Sheol h7585)
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
The womb that bore him will forget him; the worm will feed sweetly on him; he will be remembered no more; in this way, wickedness will be broken like a tree.
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
The wicked one devours the barren women who have not borne children; he does no good to the widow.
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
Yet God drags away the mighty people by his power; he rises up and does not strengthen them in life.
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
God allows them to think they are secure, and they are happy about that, but his eyes are on their ways.
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
These people are exalted; still, in only a little while, they will be gone; indeed, they will be brought low; they will be gathered up like all the others; they will be cut off like the tops of ears of grain.
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
If it is not so, who can prove me to be a liar; who can make my speech worth nothing?”

< Ayuba 24 >