< Ibraniyawa 3 >
1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Chobulyo, bakwangu banjolola, basupitwe kuliyabela zakwiwulu. Muzeze kuamana ni Jesu, mwapositola ni muprisita mukulwana utuliwamba kakwe.
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
Abakusepahala kwa Ireeza, uzo abamuketi, sina ubu nji Mushe mwa basepahalili muzubo ya Ireeza.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
Mukuti Jesu abali kusepahala hahulu mwikanya kuhita Mushe, kakuti muzaki wezubo ukutekeha hahulu kuhita izubo kasibili.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
Mukuti izubo yose izakwa muntu, kono yozaka zonse nji Ireeza.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
Kwiyaza limwi, Mushe abali muhikana yabali kusepahala mwizubo yonse ya Ireeza. Abali ipaki kuamana ni kupaka zakubusu.
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
Kono Christe Mwana njoyelele muzubo ya Ireeza. Twizubo yakwe haiba ni tukwatilila kwisepo yetu ni bwikumuso butuzumina kubuli.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Chobulyo, kwina neza sina mulutela Luhuho Lujolola: “Sunu, haiba nimuzuwa inzwi lyakwe
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
sanzi mukukutuhazi inkulo zenu sina munako zakusandukilwa, mwinako zakulikwa mwihalaupa.
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
Iyi ibali inako ibakuku ubakuku wenu habanisandukila chakunilika, imi linu, muzilimo zina makumi wone bababoni mitendo yangu. Chobulyo kananitabiswa una murahi.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Chinati, 'bahitizwe zintu zibilala mukulo zabo inako yonse. Kana babazibi inzila zangu.'
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Kuswana bulyo ni munibakokeli chakubenga kwangu: 'Kabakafwe kwinjila mwipumulo yangu.'”
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Mutokomele, bakwangu, chokuti mukati kenu sanzi kuwaniki nangati umwina winjililwa luhuho lubilala mwikulo lwakusazumina, inkulo ifutata kuzwa kwa Ireeza yohala.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
Nihakuba bulyo, mususuwezane izuba ni zuba, nihakutewa kuti nji “Sunu,” njokuti sanzi nikuwaniki mukati kenu yokukutuhazwa chakuchengelelwa chive.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
Mukuti tubabi chiyemba kwa Christe haiba ni tukwatilila kwisepo yetu itwina kwali kuzwa kutanzi kuya kumamanimani.
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
Kono inzi zibawambitwe, “Sunu, haiba nozuwa inzwi lyakwe, sanzi mukukutuhazi inkulo zenu, sina munako yabusandukili.
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
Njibani babamuzuwi Ireeza ni kumusandukila? Kahena kuti njibona babo babakazwi ni Mushe mwa Egepita?
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
Njibani babo bababengeli makumi azilimo zone? Kahena kuti njibona babo babapangi chive, basimili ifwile ibawili mwihalaupa?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
Njikubani kwabawoli kukonka kaluchi kuti ketenibawole kukenjila mupumulo yakwe?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
Imi tubona kuti kanababali kuwola kwinjila mupumulo yakwe chebaka lyakusazumina.