< Afisawa 1 >
1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
PAUL, a legate of Jesus the Messiah by the pleasure of God, to them who are at Ephesus, sanctified, and believing in Jesus the Messiah:
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Peace be with you, and grace from God our Father, and from our Lord Jesus the Messiah.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Blessed be God, the Father of our Lord Jesus the Messiah, who hath blessed us with all blessings of the Spirit in heaven, by the Messiah:
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
according as he had previously chosen us in him, before the foundation of the world, that we might be holy and without blame before him; and, in love, predestinated us for himself;
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
and adopted us for sons, in Jesus the Messiah, as was agreeable to his pleasure:
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
that the glory of his grace might be glorified, which he poured upon us by his Beloved One;
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
by whom we have redemption, and the forgiveness of sins by his blood, according to the riches of his grace,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
which hath abounded in us, in all wisdom and all spiritual understanding.
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
And he hath made us know the mystery of his pleasure, which he had before determined in himself to accomplish,
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
in the dispensation of the fullness of times; that all things might again be made new in the Messiah, things in heaven and things on earth.
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
And in him we are elected, according as he predestined us and willed, who worketh all things according to the counsel of his pleasure;
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
that we should be they who first hoped in the Messiah, to the honor of his glory.
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
In whom, ye also have heard the word of truth, which is the gospel of your life, and have believed in him; and have been sealed with the Holy Spirit, who was promised,
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
who is the earnest of our inheritance, until the redemption of them that are alive, and for the praise of his glory.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
Therefore, lo I also, since I heard of your faith in our Lord Jesus the Messiah, and of your love towards all the saints,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
cease not to give thanks on your account, and to remember you in my prayers;
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
that the God of our Lord Jesus the Messiah, the Father of glory, may give to you the Spirit of wisdom and of revelation, in the recognition of him;
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
and that the eyes of your hearts may be enlightened, so that ye may know what is the hope of his calling, and what the riches of the glory of his inheritance in the saints;
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
and what is the excellence of the majesty of his power in us who believe; according to the efficiency of the strength of his power,
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
which he put forth in the Messiah, and raised him from the dead, and seated him at his right hand in heaven,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn )
high above all principalities, and authorities, and powers, and lordships, and above every name that is named, not only in this world but also in that to come: (aiōn )
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
and he hath subjected all things under his feet; and hath given him who is high over all, to be the head of the church;
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
which is his body, and the fullness of him who filleth all in all: