< Afisawa 2 >
1 Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku.
and also you, he filleth, who were dead in your sins, and in your offences,
2 Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn )
in the which ye before walked, according to the worldliness of this world, and according to the pleasure of the prince potentate of the air, that spirit which is active in the children of disobedience: (aiōn )
3 Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah.
in which deeds we also, formerly, were conversant, in the cravings of our flesh; and we did the pleasure of our flesh, and of our mind, and were altogether the children of wrath, like the rest.
4 Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai,
But God who is rich in his mercies, because of the great love with which he loved us,
5 ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku.
when we were dead in our sins, quickened us with the Messiah, and rescued us by his grace;
6 Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya.
and resuscitated us with him, and seated us with him in heaven, in Jesus the Messiah:
7 Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn )
that he might show to the coming ages the magnitude of the riches of his grace, and his benignity towards us in Jesus the Messiah. (aiōn )
8 Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah.
For it is by his grace we are rescued, through faith; and this is not of yourselves, but it is the gift of God:
9 Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai.
not of works, lest any one glory.
10 Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.
For we are his creation; who are created in Jesus the Messiah, for good works, which God hath before prepared for us to walk in.
11 Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu).
Wherefore be mindful, that ye formerly were carnal Gentiles; and ye were called the uncircumcision, by that which is called the circumcision, and which is the work of the hands in the flesh.
12 Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah.
And ye were, at that time, without the Messiah; and were aliens from the regulations of Israel; and strangers to the covenant of the promise; and were without hope, and without God, in the world.
13 Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.
But now, by Jesus the Messiah, ye who before were afar off, have been brought near by the blood of the Messiah.
14 Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu.
For he is himself our peace, who hath made the two become one, and hath demolished the wall which stood in the midst, and the enmity, by his flesh;
15 Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu.
and by his prescriptions he hath abolished the law of ordinances; that, in himself, he might make the two to be one new man; and he hath made peace,
16 A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah.
and hath reconciled both with God, in one body, and hath slain the enmity by his cross.
17 Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa.
And he came, and proclaimed peace to you afar off, and to those near:
18 Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.
because, by him there is access for us both, by one Spirit, unto the Father.
19 Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma.
Wherefore, ye are not strangers, nor sojourners, but ye are fellow-citizens with the saints, and of the household of God.
20 Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin.
And ye are built upon the foundations of the legates and the prophets; and Jesus the Messiah hath become the head of the corner in the edifice.
21 Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji.
And in him all the edifice is framed together, and groweth into a holy temple in the Lord;
22 Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.
while ye also are builded in him, for a habitation of God through the Spirit.