< 1 Bitrus 2 >

1 Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
Etu nimite sob biya kaam khan chari dibi, aru sob thogai diya kaam aru manu logote dushmani kori thaka khan aru kiman biya bhabona monte rakhi ase eitu khan chari dibi.
2 Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
Ekta notun jonom kora bacha nisena, atma laga ekdom sapha thaka dudh nimite itcha koribi, etu pora apuni poritran pabole arubi bisi itcha koribo,
3 yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
Aru Isor kotha te likha nisina, jodi apuni Probhu to morom kore koi kene jani loise koile.
4 Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
Tai logote ahibi kun ekta jivit pathor ase, junke manu pora chari disele, kintu Isor he Taike basi loise aru bisi daam laga pathor bonaise.
5 ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
Apuni khan bhi ekta jinda thaka pathor nisena ase kunke atma laga ghor bonai dise, etu pora amikhan Isor laga pobitro kaam koribo, jeneka purohit khan kore, aru Jisu Khrista te atma laga bolidan dikena thakibo.
6 Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
Etu nimite, pobitro shastro te eneka likha ase: “Sabi, Moi Zion te kinar laga pathor hali ase, “Basi luwa aru bisi daam laga. Kun manu Taike biswas kore, tai kitia bhi sorom nakhabo.”
7 A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
Apuni khan kun biswas kore tai nimite sonman pabo. Kintu jun kotha namane, “Juntu pathor ghor bona manu khan pora phelai dise, etu he kinar laga pathor matha hoi jaise”-
8 kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
Aru “Ekta rasta bondh kori diya pathor Aru kuntu taikhan ke giribole diye.” Taikhan giri thake kelemane taikhan Isor laga kotha namane- aru etu nimite he taikhan ke bachi loise.
9 Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
Kintu apuni ekjon basi luwa manu khan ase, ekta purohit rajyo, ekta pobitro desh, Isor laga nijor manu khan, etu pora apuni khan Tai laga asurit kaam khan dusra ke koi dibo, Tai jun pora apuni khan ke andhera pora mati kene ujala te loi anise.
10 Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
Ek homoi te apuni khan Tai laga manu thaka nai, Kintu etiya apuni khan Isor laga manu hoi jaise. Apuni khan poila te daya panai, Kintu etiya to daya paise.
11 Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
Morom laga bhai khan, moi pora apuni khan to dusra desh laga manu thaka nisena, mangso laga itcha pora dur thaki bole nimite mati ase, kun pora apuni laga atma logot lorai kori ase.
12 Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
Porjati khan logote apuni khan bhal kaam kori kene dikhai dibi, etu pora jodi taikhan apuni pora biya kaam kori thaka nisena kotha kore, taikhan apuni laga bhal kaam to dikhibo aru Isor aha laga dinte Taike mohima dibo.
13 Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
Manu pora ki adhikar cholai ase etu Probhu nimite mani kene thakibi. Prithibi laga raja khan ke mani kene thakibi,
14 ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
Aru Governor khan ke, kun Tai pora pathaise biya kaam kora khan ke saja dibole nimite, aru kun bhal kaam kore taikhan ke prosansa koribo nimite.
15 Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
Kelemane etu Isor laga itcha ase, etu pora apuni ki bhal kaam kori ase etu dikhi kene kaam nathaka murkho khan laga kotha ke chup kori dibo.
16 Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
Ekjon ajad manu nisena, apuni laga ajadi ke biya kaam lukai dibole nimite nacholabi, kintu Isor laga noukar nisena thakibi.
17 Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
Sob manu ke sonman koribi. Bhai kokai khan ke morom thaki bole itcha koribi. Isor ke bhoi koribi. Aru raja ke sonman koribi.
18 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
Nokorkhan, malik ke sob kaam pora sewa koribi. Khali bhal aru morom kora malik ke he sewa nakori bhi, kintu khechera malik hoilebi taike sewa koribi.
19 Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
Kelemane etu bisi asis kotha ase ekjon nimite jodi tai logote anyai hoi thaka nimite dukh digdar pai thakile bhi, tai kaam khan kori thake, kele koile tai Isor ke jani loise.
20 Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
Apuni khan laga ki labh ase jodi apuni paap kori kene aru etu laga sajah bhi pai? Kintu jodi apuni bhal kaam kori kene sajah pa homoi te dukh pai, eneka korile he apuni Isor usorte mohima pabole yogya ase.
21 Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
Kelemane etu nimite he apuni ke matise, aru Khrista bhi apuni nimite dukh paise. Tai laga jibon pora apuni khan bhal rasta te bera bole nimite dikhai dise.
22 “Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
“Tai eku paap kaam kora nai, Aru Tai laga mukh pora kitia bhi biya kotha ula nai.”
23 Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
Jitia Jisu Khrista ke biya kotha khan koisele, Tai wapas taikhan ke biya kotha koi kene jawab diya nai. Jitia Tai dukh paise, Taikhan ke wapas dukh pabole nimite dhomki diya nai, kintu Tai kun bhal pora bisar kore taike nijor jibon to di dise.
24 Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
Tai amikhan laga paap to uthaikene nijor gaw to Cross te mori bole dise, etu pora amikhan paap te eku bhag nathakibole nimite, aru amikhan dharmik jibon loi kene jinda thakibo. Tai laga ghaw pora amikhan changai paise.
25 Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.
Kelemane apuni khan harai ja mer nisena berai thakise, kintu etiya apuni mer rokhiya logote wapas ahi jaise aru apuni khan laga atma ke bachai diya malik usorte ahise.

< 1 Bitrus 2 >