Aionian Verses
Genesis 37:35 (Farawa 37:35)
(parallel missing)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol )
Genesis 42:38 (Farawa 42:38)
(parallel missing)
Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol )
Genesis 44:29 (Farawa 44:29)
(parallel missing)
In kun ɗauki wannan daga wurina shi ma wani abu ya same shi, za ku kawo furfura kaina zuwa kabari cikin baƙin ciki.’ (Sheol )
Genesis 44:31 (Farawa 44:31)
(parallel missing)
ya ga cewa saurayin ba ya nan, zai mutu. Bayinka za su sa bawanka, mahaifinmu, yă mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. (Sheol )
Numbers 16:30 (Ƙidaya 16:30)
(parallel missing)
Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
Numbers 16:33 (Ƙidaya 16:33)
(parallel missing)
Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
Deuteronomy 32:22 (Maimaitawar Shari’a 32:22)
(parallel missing)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol )
1 Samuel 2:6 (1 Sama’ila 2:6)
(parallel missing)
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol )
2 Samuel 22:6 (2 Sama’ila 22:6)
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
1 Kings 2:6 (1 Sarakuna 2:6)
(parallel missing)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol )
1 Kings 2:9 (1 Sarakuna 2:9)
(parallel missing)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol )
Job 7:9 (Ayuba 7:9)
(parallel missing)
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
Job 11:8 (Ayuba 11:8)
(parallel missing)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
Job 14:13 (Ayuba 14:13)
(parallel missing)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol )
Job 17:13 (Ayuba 17:13)
(parallel missing)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
Job 17:16 (Ayuba 17:16)
(parallel missing)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
Job 21:13 (Ayuba 21:13)
(parallel missing)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
Job 24:19 (Ayuba 24:19)
(parallel missing)
Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol )
Job 26:6 (Ayuba 26:6)
(parallel missing)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
Psalms 6:5 (Zabura 6:5)
(parallel missing)
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
Psalms 9:17 (Zabura 9:17)
(parallel missing)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
Psalms 16:10 (Zabura 16:10)
(parallel missing)
domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol )
Psalms 18:5 (Zabura 18:5)
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Psalms 30:3 (Zabura 30:3)
(parallel missing)
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
Psalms 31:17 (Zabura 31:17)
(parallel missing)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol )
Psalms 49:14 (Zabura 49:14)
(parallel missing)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
Psalms 49:15 (Zabura 49:15)
(parallel missing)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
Psalms 55:15 (Zabura 55:15)
(parallel missing)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
Psalms 86:13 (Zabura 86:13)
(parallel missing)
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
Psalms 88:3 (Zabura 88:3)
(parallel missing)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
Psalms 89:48 (Zabura 89:48)
(parallel missing)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
Psalms 116:3 (Zabura 116:3)
(parallel missing)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
Psalms 139:8 (Zabura 139:8)
(parallel missing)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
Psalms 141:7 (Zabura 141:7)
(parallel missing)
Za su ce, “Kamar yadda mutum kan yi huda yă tsage ƙasa, haka aka watsar da ƙasusuwanmu a bakin kabari.” (Sheol )
Proverbs 1:12 (Karin Magana 1:12)
(parallel missing)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
Proverbs 5:5 (Karin Magana 5:5)
(parallel missing)
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
Proverbs 7:27 (Karin Magana 7:27)
(parallel missing)
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )
Proverbs 9:18 (Karin Magana 9:18)
(parallel missing)
Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol )
Proverbs 15:11 (Karin Magana 15:11)
(parallel missing)
Mutuwa da Hallaka suna nan a fili a gaban Ubangiji, balle fa zukatan mutane! (Sheol )
Proverbs 15:24 (Karin Magana 15:24)
(parallel missing)
Hanyar rai na yin jagora ya haura wa masu hikima don ta kiyaye shi daga gangarawa zuwa kabari. (Sheol )
Proverbs 23:14 (Karin Magana 23:14)
(parallel missing)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
Proverbs 27:20 (Karin Magana 27:20)
(parallel missing)
Mutuwa da Hallaka ba sa ƙoshi, haka idanun mutum ba sa ƙoshi da gani. (Sheol )
Proverbs 30:16 (Karin Magana 30:16)
(parallel missing)
Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol )
Ecclesiastes 9:10 (Mai Hadishi 9:10)
(parallel missing)
Duk abin da hannunka yake yi, ka yi shi da dukan ƙarfinka, gama a cikin kabari in da za ka, babu aiki ko shirye-shirye, ko sani, ko hikima. (Sheol )
Song of Solomon 8:6 (Waƙar Waƙoƙi 8:6)
(parallel missing)
Ka sa ni kamar hatimi a zuciyarka, kamar hatimi a hannunka; gama ƙauna tana da ƙarfi kamar mutuwa, kishinta yana kamar muguntar kabari, yana ƙuna kamar wuta mai ci, kamar gagarumar wuta. (Sheol )
Isaiah 5:14 (Ishaya 5:14)
(parallel missing)
Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka; cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu. (Sheol )
Isaiah 7:11 (Ishaya 7:11)
(parallel missing)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol )
Isaiah 14:9 (Ishaya 14:9)
(parallel missing)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol )
Isaiah 14:11 (Ishaya 14:11)
(parallel missing)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol )
Isaiah 14:15 (Ishaya 14:15)
(parallel missing)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol )
Isaiah 28:15 (Ishaya 28:15)
(parallel missing)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
Isaiah 28:18 (Ishaya 28:18)
(parallel missing)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
Isaiah 38:10 (Ishaya 38:10)
(parallel missing)
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
Isaiah 38:18 (Ishaya 38:18)
(parallel missing)
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
Isaiah 57:9 (Ishaya 57:9)
(parallel missing)
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
Ezekiel 31:15 (Ezekiyel 31:15)
(parallel missing)
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol )
Ezekiel 31:16 (Ezekiyel 31:16)
(parallel missing)
Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol )
Ezekiel 31:17 (Ezekiyel 31:17)
(parallel missing)
Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol )
Ezekiel 32:21 (Ezekiyel 32:21)
(parallel missing)
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol )
Ezekiel 32:27 (Ezekiyel 32:27)
(parallel missing)
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol )
Hosea 13:14 (Hosiya 13:14)
(parallel missing)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
Amos 9:2
(parallel missing)
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol )
Jonah 2:2 (Yunana 2:2)
(parallel missing)
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol )
Habakkuk 2:5
(parallel missing)
ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
But I say to you, That every one who is angry with his brother rashly, is obnoxious to judgment: and every one that saith to his brother, Raka! is obnoxious to the council: and every one that shall say, Fool is obnoxious to hell-fire. (Geenna )
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna )
If therefore thy right eye make thee offend, pluck it out, and cast it from thee; because it is better for thee that thy one member perish, than that thy whole body fall into hell. (Geenna )
In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
And if thy right hand make thee offend, cut it off, and cast it from thee; because it is better for thee that one of thy members perish, than that thy whole body fall into hell. (Geenna )
In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
And be not afraid of them that kill the body, but cannot kill the soul; but be afraid rather of Him who can destroy both soul and body in hell. (Geenna )
Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna )
And thou, Capernaum, which hast been lifted up to heaven, shalt be brought down to the grave. For if those deeds of power which were done in thee, had been done in Sodom, it would have stood to this day. (Hadēs )
Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. (Hadēs )
And whoever shall speak a word against the Son of man, it will be forgiven him: but whoever shall speak against the Holy Spirit, it will not be forgiven him; not in this world, and not in the world to come. (aiōn )
Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn )
And that which was sowed among thorns, is he that heareth the word; and care for this world and the deceptiveness of riches, choke the word; and he is without fruits. (aiōn )
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
The enemy that sowed them, is Satan. The harvest is the end of the world: and the reapers are the angels. (aiōn )
abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
As therefore the tares are gathered and burned in the fire; so will it be in the end of the world. (aiōn )
“Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
So will it be in the end of the world. The angels will go forth, and will sever the wicked from among the just; (aiōn )
Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
Also I say to thee, that thou art Cephas: and upon this rock, I will build my church: and the gates of death shall not triumph over it. (Hadēs )
Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs )
If then thy hand or thy foot make thee stumble, cut it off and cast it from thee: for it is good for thee to enter into life lame or mutilated, and not that, with two hands or two feet, thou fall into eternal fire. (aiōnios )
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios )
And if thine eye make thee stumble, pluck it out and cast it from thee: for it is good for thee to enter into life with one eye, and not that, with two eyes, thou fall into the hell of fire. (Geenna )
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna )
And one came, drew near, and said to him: Good Teacher, what good thing must I do, that eternal life may be mine? (aiōnios )
To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
And every man that relinquisheth houses, or brothers or sisters, or father or mother, or wife or children, or lands, for my name's sake, shall receive an hundredfold, and shall inherit eternal life. (aiōnios )
Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
And he saw a fig-tree by the way, and came to it and found nothing on it, except leaves only. And he said to it: There shall no more be fruit on thee for ever. And immediately the fig-tree withered. (aiōn )
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn )
Woe to you, Scribes and Pharisees, hypocrites: for ye traverse sea and land to make one proselyte; and when he is gained, ye make him a child of hell twofold more than yourselves. (Geenna )
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna )
Ye serpents, ye race of vipers: how can ye escape the condemnation of hell? (Geenna )
“Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna )
And as Jesus sat on the mount of Olives, his disciples came, and said between themselves and him: Tell us when these things are to be; and what will be the sign of thy coming, and of the consummation of the world. (aiōn )
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
Then will he say also to them on his left hand: Go from me, ye accursed, into everlasting fire, which was prepared for the Calumniator and his angels, (aiōnios )
“Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios )
And these will go into everlasting torment, and the righteous into everlasting life. (aiōnios )
“Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios )
And teach them to observe all that I have commanded you. And, behold, I am with you always, unto the consummation of the worlds Amen. Completion of the Holy Gospel as published by Matthew; and which he published in Hebrew, in the land of the Palestineans. (aiōn )
kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn )
but whoever shall blaspheme against the Holy Spirit, to him for ever there is no forgiveness; but he is obnoxious to eternal judgment. (aiōn , aiōnios )
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn , aiōnios )
and the cares of this world, and the deceitfulness of riches, and the residue of other lusts enter in and choke the word, and it is without fruits. (aiōn )
amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
And if thy hand make thee offend, cut it off: it is better for thee to enter into life maimed, than, having two hands, to go into hell; (Geenna )
In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
And if thy foot make thee offend, cut it off: it is better for thee to enter into life lamed, than, having two feet, to fall into hell; (Geenna )
In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
And if thy eye make thee offend, pluck it out: it is better for thee to enter with one eye into the kingdom of God, than, having two eyes, to fall into the hell of fire; (Geenna )
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
And as he walked in the way, one ran and fell upon his knees, and asked him, and said: Good Teacher, what must I do, to inherit eternal life? (aiōnios )
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
who will not receive a hundredfold, here in the present time, houses, and brothers and sisters, and mothers and children, and lands, with persecution; and in the world to come eternal life. (aiōn , aiōnios )
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
And he said to it: Henceforth and for ever, let no man eat fruit from thee: and the disciples heard it. And they came to Jerusalem. (aiōn )
Sai ya ce wa itacen, “Kada kowa yă ƙara cin’ya’yanka.” Almajiransa kuwa suka ji ya faɗi haka. (aiōn )
And he will reign over the house of Jacob for ever; and of his reign there will be no end. (aiōn )
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
(as he spoke with the fathers, ) with Abraham and his seed, for ever. (aiōn )
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
as he spake by the mouth of his holy prophets, who were of old, (aiōn )
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
And they besought him, not to command them to depart into the abyss. (Abyssos )
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos )
And thou Capernaum, that art lifted up to heaven, shalt be brought down to hell. (Hadēs )
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
And behold, a Scribe stood up to try him, and said: Teacher, what must I do, to inherit eternal life? (aiōnios )
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
But I will show you, of whom to be afraid: of him who, after he hath killed, hath authority to cast into hell. Yea, say I to you: be afraid of him. (Geenna )
Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna )
And our Lord praised the unrighteous steward, for having acted sagaciously: for the children of this world are more sagacious than the children of light, in this their generation. (aiōn )
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn )
And I also say to you: Make to yourselves friends, with this unrighteous mammon; so that when it is finished, they may receive you to their everlasting tabernacles. (aiōnios )
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios )
And being tormented in hell, he raised his eyes from afar off, and saw Abraham, and Lazarus in his bosom. (Hadēs )
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs )
And one of the chiefs asked him, and said to him: Good Teacher, what shall I do, that I may inherit eternal life? (aiōnios )
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
that shall not receive manifold in the present time, and, in the coming world, eternal life. (aiōn , aiōnios )
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn , aiōnios )
Jesus said to them: The children of this world take wives, and wives are given to husbands. (aiōn )
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn )
But they who are worthy of that world, and of the resurrection from the dead, do not take wives, nor are wives given to husbands. (aiōn )
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn )
that every one who believeth in him, may not perish, but may have life eternal. (aiōnios )
don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios )
For God so loved the world, that he gave his only begotten Son, that whosoever believeth on him, should not perish, but should have life eternal. (aiōnios )
Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios )
He that believeth on the Son, hath life eternal; but he who obeyeth not the Son, shall not see life. but the wrath of God will abide upon him. (aiōnios )
Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios )
but whoever shall drink of the waters which I shall give him, will not thirst for ever; but the waters, which I shall give him, will be in him a fountain of waters, springing up unto life eternal. (aiōn , aiōnios )
amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn , aiōnios )
And he that reapeth, receiveth wages, and gathereth fruits unto life eternal; and the sower and the reaper equally rejoice. (aiōnios )
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios )
Verily, verily, I say to you, That he who heareth my word, and believeth on him that sent me, hath life eternal, and will not come into condemnation, but hath passed from death to life. (aiōnios )
“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Search the scriptures; for in them, ye think, there is life eternal for you; and they testify of me. (aiōnios )
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
Labor not for the food that perisheth, but for the food that abideth unto life eternal, which the Son of man will give to you; for him hath God the Father sealed. (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
For this is the pleasure of my Father, that every one who seeth the Son, and believeth on him, should have life eternal; and I will raise him up at the last day. (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
Verily, verily, I say to you: That, to him who believeth in me, there is life eternal. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
I am the bread of life, who have come down from heaven: and if a man shall eat of this bread, he will live for ever. And the bread which I shall give, is my body, which I give for the life of the world. (aiōn )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
But he that eateth of my body, and drinketh of my blood, to him is life eternal; and I will raise him up at the last day (aiōnios )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
This is the bread that came down from heaven: not as your fathers ate the manna, and died; whoever shall eat of this bead, will live for ever. (aiōn )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
Simon Cephas replied, and said: My Lord, to whom shall we go? The words of life eternal are with thee. (aiōnios )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
And a servant abideth not for ever in the house; but the Son abideth for ever. (aiōn )
Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn )
Verily, verily, I say to you: He that keepeth my word, will never see death. (aiōn )
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn )
The Jews say to him: Now we know, that thou hast a demon. Abraham is dead, and the prophets; yet thou sayest: He that keepeth my word, will never taste death. (aiōn )
Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn )
Never hath it been heard, that any one opened the eyes of one born blind. (aiōn )
Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
And I give to them life eternal: and they will never be lost: nor will any one pluck them from my hand. (aiōn , aiōnios )
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
And every one that liveth, and believeth in me, will not die for ever. Believest thou this? (aiōn )
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn )
He that loveth his life, will lose it; and he that hateth his life, in this world, will preserve it unto life everlasting. (aiōnios )
Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios )
The multitude said to him: We have heard from the law, that the Messiah abideth for ever: and how sayest thou, that the Son of man is to be lifted up? Who is this Son of man? (aiōn )
Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn )
And I know that his commandment is life eternal. Therefore, these things which I speak, as my Father hath said to me, so I speak. (aiōnios )
Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios )
Simon Cephas said to him: Never shalt thou wash my feet. Jesus said to him: Unless I wash thee, thou hast no part with me. (aiōn )
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
And I will ask of my Father, and he will give you another Comforter, that he may be with you for ever, (aiōn )
Zan kuwa roƙi Uba, zai kuwa ba ku wani Mai Taimakon da zai kasance tare da ku har abada, (aiōn )
As thou hast given him authority over all flesh, that he might give life eternal to as many as thou hast given him. (aiōnios )
Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios )
And this is life eternal, that they may know thee, that thou art the only true God, and whom thou hast sent, Jesus Messiah. (aiōnios )
Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios )
For thou wilt not leave my soul in the grave, nor wilt thou give thy pious one to see corruption. (Hadēs )
gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
And he foresaw, and spoke of the resurrection of Messiah, that he was not left in the grave, neither did his body see corruption. (Hadēs )
Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
whom the heavens must retain, until the completion of the times of those things, which God hath spoken by the mouth of his holy prophets of old. (aiōn )
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
And Paul and Barnabas said openly: To you first, ought the word of God to be spoken; but because ye repel it from you, and decide, against yourselves, that ye are not worthy of life eternal, lo, we turn ourselves to the Gentiles. (aiōnios )
Sai Bulus da Barnabas suka amsa musu gabagadi, suka ce, “Ya zama mana dole mu yi muku maganar Allah da farko. Da yake kun ƙi ta ba ku kuma ga kun cancanci rai madawwami ba, to, za mu juya ga Al’ummai. (aiōnios )
And when the Gentiles heard this, they rejoiced and glorified God. And those believed, who were appointed to life eternal. (aiōnios )
Sa’ad da Al’ummai suka ji haka, sai suka yi farin ciki suka ɗaukaka maganar Ubangiji; kuma duk waɗanda aka zaɓa don samun rai madawwami, suka gaskata. (aiōnios )
Known, from of old, are the works of God. (aiōn )
da aka sani tun zamanai. (aiōn )
For, from the foundations of the world, the occult things of God are seen, by the intellect, in the things he created, even his eternal power and divinity; so that they might be without excuse; (aïdios )
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios )
And they changed the truth of God into a lie; and worshipped and served the created things, much more than the Creator of them, to whom belong glory and blessing, for ever and ever: Amen. (aiōn )
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn )
to them who, by perseverance in good works, seek for glory and honor and immortality, to them he will give life eternal; (aiōnios )
Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. (aiōnios )
So that, as sin had reigned in death, so grace might reign in righteousness unto life eternal, by means of our Lord Jesus Messiah. (aiōnios )
domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios )
And now, as ye have been emancipated from sin, and have become servants to God, your fruits are holy; and the result thereof is life everlasting. (aiōnios )
Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios )
For the wages of sin is death; but the free gift of God is life eternal, through our Lord Jesus Messiah. (aiōnios )
Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios )
and from among whom, Messiah appeared in the flesh, who is God over all; to whom be praises and benediction, for ever and ever; Amen. (aiōn )
Kakannin-kakannin nan kuma nasu ne, Kiristi kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo ya tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome! Amin. (aiōn )
Or, Who descendeth to the abyss of the grave, and bringeth up Messiah from the place of the dead? (Abyssos )
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos )
For God hath shut up all men in disobedience, that upon all men he might have mercy. (eleēsē )
Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē )
Because, all is from him, and all by him, and all through him: to whom be praises and benedictions, for ever and ever: Amen. (aiōn )
Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn )
And be not conformed to this world; but be ye transformed, by the renovation of your minds: and discern ye what is the good and acceptable and perfect pleasure of God. (aiōn )
Kada ku ci gaba da yin abin da duniya take yi, sai dai ku bar halinku ya sāke, ta wurin sabunta hankalinku ɗungum, don ku tabbatar da abin da Allah yake so yake, abu mai kyau, mai daɗi da kuma cikakke. (aiōn )
Now unto God, who is able to establish you, - (according to my gospel, which is proclaimed concerning Jesus Messiah; and according to the revelation of the mystery, which was hidden from the times that are past, (aiōnios )
Ɗaukaka ta tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa’azin Yesu Kiristi, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil azal, (aiōnios )
but is at this time revealed, by means of the scriptures of the prophets; and by the command of the eternal God, is made known to all the Gentiles, for the obedience of faith; ) (aiōnios )
amma yanzu kuwa aka bayyana, aka kuma sanar ta wurin rubuce-rubucen annabawa bisa ga umarnin Allah madawwami, domin dukan al’ummai su gaskata su kuma yi masa biyayya (aiōnios )
to him who only is wise, be glory, through Jesus Messiah, for ever and ever: Amen. (aiōn )
ɗaukaka ta tabbata har abada ga Allah, wanda shi ne kaɗai mai hikima ta wurin Yesu Kiristi! Amin. (aiōn )
Where is the wise? Or where is the scribe? Or where is the disputant of this world? Lo, hath not God showed, that the wisdom of this world is folly? (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
Yet we do speak wisdom, among the perfect; the wisdom not of this world, nor of the potentates of this world, who will come to naught. (aiōn )
Duk da haka, muna sanar da saƙon hikima cikin waɗanda suka balaga, amma ba hikima irin ta wannan zamani ba ne, ko kuwa irin ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda za su shuɗe ba. (aiōn )
But we speak the wisdom of God, in a mystery; the wisdom which was hidden, and which God predetermined before the world was, for our glory: (aiōn )
A’a, muna magana ne a kan asirin hikimar Allah, hikimar da tun dā, take a ɓoye, wadda Allah ya ƙaddara domin ɗaukakarmu, tun kafin farkon zamanai. (aiōn )
which no one of the potentates of this world knew; for had they known it, they would not have crucified the Lord of glory. (aiōn )
Ba ko ɗaya daga cikin masu mulkin wannan zamani da ya fahimce ta, gama da a ce sun fahimce ta, da ba su gicciye Ubangiji mai ɗaukaka ba. (aiōn )
Let no one deceive himself. Whoever among you thinketh that he is wise in this world, let him become a fool, that he may be wise. (aiōn )
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
Wherefore, if food is a stumbling-block to my brother, I will for ever eat no flesh, lest I should be a stumbling-block to my brother. (aiōn )
Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe. (aiōn )
All these things which befell them, were for an example to us; and they are written for our instruction, on whom the end of the world hath come. (aiōn )
Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn )
Where is thy sting, O death? And where is thy victory, O grave? (Hadēs )
“Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
to them whose minds the God of this world hath blinded, in order that they might not believe, lest the light of the gospel of the glory of the Messiah (who is the likeness of God) should dawn upon them. (aiōn )
Allahn zamanin nan ya makanta hankulan marasa ba da gaskiya, yadda har ba za su iya ganin hasken bishara ta ɗaukakar Kiristi ba, wanda yake kamannin Allah. (aiōn )
For the affliction of the present time, though very small and light, prepareth for us great glory, without end, for ever and ever; (aiōnios )
Don wannan’yar wahalar tamu mai saurin wucewa, ita take tanadar mana madawwamiyar ɗaukaka mai yawa, fiye da kwatanci. (aiōnios )
while we look not at these seen things, but at those not seen; for these seen things are temporary, but those not seen are eternal. (aiōnios )
Domin ba abubuwan da ido yake gani ne muke dubawa ba, sai dai marasa ganuwa. Gama abubuwan da ake gani masu saurin wucewa ne, marasa ganuwa kuwa, madawwama ne. (aiōnios )
For we know that, if our house on earth-this of the body, were dissolved, yet we have a building of God, a house not made with hands, eternal in heaven. (aiōnios )
Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios )
As it is written, He hath dispersed and given to the poor; and his righteousness is established for ever. (aiōn )
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ya ba gajiyayyu hannu sake, ayyukansa na alheri madawwama ne.” (aiōn )
God, the Father of our Lord Jesus the Messiah, blessed for ever and ever, he knoweth that I lie not. (aiōn )
Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn )
who gave himself for our sins, that he might deliver us from this evil world, agreeably to the pleasure of God our Father: (aiōn )
Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
He who soweth in the flesh, reapeth from the flesh corruption: and he who soweth in the Spirit, will from the Spirit reap life everlasting. (aiōnios )
Wanda ya yi shuki don yă gamshi mutuntakarsa, daga wannan mutuntaka zai girbi hallaka. Wanda ya yi shuki domin yă gamshi Ruhu, daga Ruhu zai girbi rai madawwami. (aiōnios )
high above all principalities, and authorities, and powers, and lordships, and above every name that is named, not only in this world but also in that to come: (aiōn )
Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn )
in the which ye before walked, according to the worldliness of this world, and according to the pleasure of the prince potentate of the air, that spirit which is active in the children of disobedience: (aiōn )
Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn )
that he might show to the coming ages the magnitude of the riches of his grace, and his benignity towards us in Jesus the Messiah. (aiōn )
Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn )
and should show to all men what is the dispensation of the mystery, which for ages was hid up in God the Creator of all things: (aiōn )
An zaɓe ni in bayyana wa dukan mutane shirin asirin nan wanda Allah, mahaliccin kome, ya ɓoye shekara da shekaru. (aiōn )
which wisdom he arranged ages before, and he hath executed it by Jesus the Messiah our Lord; (aiōn )
Wannan shi ne madawwamin shirinsa, kuma an aikata shi ta wurin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōn )
to him be glory, in his church, by Jesus the Messiah, in all generations, for ever and ever. Amen. (aiōn )
Bari ɗaukaka ta tabbata a gare shi a cikin ikkilisiya da kuma a cikin Kiristi Yesu, har yă zuwa dukan zamanai, har abada abadin! Amin. (aiōn )
For our conflict is not with flesh and blood, but with principalities, and with those in authority, and with the possessors of this dark world, and with the evil spirits that are beneath heaven. (aiōn )
Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. (aiōn )
And to God our Father, be glory and honor, for ever and ever. Amen. (aiōn )
Ɗaukaka ta tabbata ga Allahnmu da Ubanmu har abada abadin. Amin. (aiōn )
namely, that mystery, which was hidden for ages and generations, but is now revealed to his saints; (aiōn )
Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn )
For these will be recompensed with the judgment of eternal destruction, from the presence of our Lord, and from the glory of his power; (aiōnios )
Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios )
And may our Lord Jesus the Messiah himself, and God our Father, who hath loved us, and given us everlasting consolation and a good hope through his grace, (aiōnios )
Ubangijinmu Yesu Kiristi kansa da kuma Allah Ubanmu, wanda ya ƙaunace mu kuma ta wurin alherinsa yă ba mu madawwamiyar ƙarfafawa da kyakkyawar bege, (aiōnios )
But for this cause had he mercy on me, that in me first Jesus the Messiah might display all his long suffering, for an example to them who were to believe on him unto life eternal. (aiōnios )
Amma saboda wannan dalilin ne aka nuna mini jinƙai domin ta wurina, mafi zunubi duka, Kiristi Yesu yă iya bayyana matuƙar haƙurinsa a matsayin misali ga waɗanda za su gaskata shi su kuma sami rai madawwami. (aiōnios )
And to the king eternal, incorruptible, and invisible, the sole God, be honor and glory for ever and ever! Amen. (aiōn )
Bari girma da ɗaukaka su tabbata har abada abadin ga Sarki madawwami, wanda ba ya mutuwa, wanda ba a ganinsa, wanda kuma shi ne kaɗai Allah! Amin. (aiōn )
And contend in the good contest of faith; and lay hold of life eternal, to which thou art called, and of which thou hast confessed a good confession before many witnesses. (aiōnios )
Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios )
who only is incorruptible, and dwelleth in light to which no one can approach; and whom no man hath seen, or even can see: to him be glory and dominion for ever and ever. Amen. (aiōnios )
wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios )
Charge the rich of this world, that they be not uplifted in their minds; and that they confide not in riches, in which is no security; but in the living God, who giveth us all things abundantly for our comfort: (aiōn )
Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn )
who hath vivified us, and called us with a holy calling; not according to our works, but according to his good pleasure, and his grace that was given us in Jesus the Messiah from time before the ages, (aiōnios )
wanda ya cece mu ya kuma kira mu ga rayuwar tsarki ba saboda wani abin da muka yi ba sai dai saboda nufinsa da kuma alherinsa. An ba mu wannan alheri cikin Kiristi Yesu tun fil azal, (aiōnios )
Therefore I endure every thing, for the elect's sake; that they also may obtain life, in Jesus the Messiah, with eternal glory. (aiōnios )
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
For Demas hath left me; and hath loved this world and gone away to Thessalonica; Crispus to Galatia, Titus to Dalmatia. (aiōn )
gama Demas, saboda ƙaunar wannan duniya, ya yashe ni ya tafi Tessalonika. Kirssens ya tafi Galatiya, Titus kuwa ya tafi Dalmatiya. (aiōn )
And my Lord will rescue me from every evil work; and will give me life in his heavenly kingdom. To him be glory, for ever and ever. Amen. (aiōn )
Ubangiji zai cece ni daga kowane mugun hari yă kuma kai ni mulkinsa na sama lafiya. A gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
concerning the hope of eternal life, which the veracious God promised before the times of the world; (aiōnios )
duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, (aiōnios )
and it teacheth us, to deny ungodliness and worldly lusts, and to live in this world in sobriety, and in uprightness, and in the fear of God, (aiōn )
Yana koya mana mu ce, “A’a” ga rashin tsoron Allah da kuma sha’awace-sha’awacen duniya, mu kuma yi rayuwa ta kamunkai, ta adalci da kuma ta tsoron Allah a cikin wannan zamani, (aiōn )
that we might be justified by his grace, and become heirs in the hope of eternal life. (aiōnios )
wannan fa domin an kuɓutar da mu ne ta wurin alherinsa, don mu zama magāda masu begen ga rai madawwami. (aiōnios )
And, perhaps, also, he therefore departed from thee for a season, that thou mightest retain him for ever; (aiōnios )
Wataƙila abin da ya sa aka raba ka da shi na ɗan lokaci ƙanƙani shi ne don ka same shi da amfani (aiōnios )
But in these latter days, he hath conversed with us, by his Son; whom he hath constituted heir of all things, and by whom he made the worlds; (aiōn )
amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
But of the Son he said: Thy throne, O God, is for ever and ever; a righteous sceptre is the sceptre of thy kingdom. (aiōn )
Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
As he said also in another place: Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
And thus he was perfected and became the cause of eternal life to all them who obey him. (aiōnios )
kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios )
and for the doctrine of baptism, and for the laying on of a hand, and for the resurrection from the dead, and for the eternal judgment? (aiōnios )
Kuma bai kamata mu ci gaba da koyar da umarnai game da baftisma, ɗibiya hannuwa, tashin matattu, da kuma madawwamin hukunci ba. (aiōnios )
and have tasted the good word of God, and the power of the world to come, (aiōn )
waɗanda suka ɗanɗana daɗin maganar Allah da kuma ikokin zamani mai zuwa, (aiōn )
whither Jesus hath previously entered for us, and hath become a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
inda Yesu, wanda ya sha gabanmu, ya shiga a madadinmu. Ya zama babban firist na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek. (aiōn )
For he testified of him: Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
For they became priests without an oath; but this man by an oath. As he said to him by David: The Lord hath sworn, and will not lie, Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
shi wannan ya zama firist ta wurin rantsuwar da Allah ya yi da ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, ba kuwa zai canja zuciyarsa ba, ‘Kai firist ne na har abada.’” (aiōn )
but this man, because he standeth up for ever, his priesthood doth not pass away: (aiōn )
amma Yesu ba zai mutu ba, don haka zai zama firist har abada. (aiōn )
For the law constituted feeble men priests; but the word of the oath, which was subsequent to the law constituted the Son perfect for ever. (aiōn )
Gama doka takan naɗa babban firist a cikin mutane masu kāsawa; amma rantsuwar da ta zo bayan dokar, ta naɗa Ɗan, wanda aka mai da shi cikakke har abada. (aiōn )
And he did not enter with the blood of goats and calves; but with the blood of himself, he entered once into the sanctuary, and obtained eternal redemption. (aiōnios )
Bai shiga ta wurin jinin awaki da na maruƙa ba; amma ya shiga Wuri Mafi Tsarki sau ɗaya tak ta wurin jininsa, bayan ya samo madawwamiyar fansa. (aiōnios )
then how much more will the blood of the Messiah, who by the eternal Spirit offered himself without blemish to God, purge our conscience from dead works, so that we may serve the living God? (aiōnios )
balle jinin Kiristi, wanda ta wurin Ruhu madawwami ya miƙa kansa marar aibi ga Allah, ai, zai tsabtacce lamirinmu daga ayyukan da suke kai ga mutuwa, don mu bauta wa Allah mai rai! (aiōnios )
And for this reason he became the Mediator of the new covenant, that he might by his death be redemption, to them who had transgressed the first covenant; so that they, who are called to the eternal inheritance, might receive the promise. (aiōnios )
Saboda haka Kiristi shi ne matsakancin sabon alkawari, don waɗanda aka kira su sami madawwamin gādon da aka yi alkawari, yanzu da ya mutu a matsayin mai fansa don yă’yantar da su daga zunuban da aka aikata a ƙarƙashin alkawari na farko. (aiōnios )
otherwise, he must have suffered many times, since the commencement of the world; but now in the end of the world, he hath once offered himself in a self-sacrifice, to abolish sin. (aiōn )
Da a ce haka ne, ai, da Kiristi ya sha wahala sau da yawa tun halittar duniya. Amma yanzu ya bayyana sau ɗaya tak a ƙarshen zamanai domin yă kawar da zunubi ta wurin miƙa kansa hadaya. (aiōn )
For by faith, we understand that the worlds were framed by the word of God; and that things seen, originated from those that are not seen. (aiōn )
Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn )
Jesus the Messiah is the same, yesterday, to-day, and for ever. (aiōn )
Yesu Kiristi ba ya sākewa, shi ne a jiya, shi ne a yau, shi ne kuma har abada. (aiōn )
May the God of peace, who brought up from the dead the great Shepherd of the flock, by the blood of the everlasting covenant, namely Jesus the Messiah, our Lord, (aiōnios )
Bari Allah na salama, wanda ta wurin jinin madawwamin alkawari ya tā da Ubangijinmu Yesu daga matattu, wannan Makiyayin tumaki mai girma, (aiōnios )
make you perfect in every good work, that ye may do his pleasure; and himself operate in you that which is pleasing In his sight, through Jesus the Messiah; to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
yă kintsa ku da kowane abu mai kyau domin aikata nufinsa, bari kuma yă aikata abin da zai gamshe shi cikinmu, ta wurin Yesu Kiristi, a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn )
Now the tongue is a fire, and the world of sin is like a forest. And this tongue, which is one among our members, marreth our whole body; and it inflameth the series of our generations that roll on like a wheel; and it is itself on fire. (Geenna )
Harshe ma wuta ne! A cikin duk gaɓoɓinmu, harshe shi ne tushen kowace irin mugunta, mai ɓata mutum gaba ɗaya, mai zuga zuciyar mutum ta tafasa, shi kuwa jahannama ce take zuga shi. (Geenna )
like persons born again, not of seed that perisheth, but of that which doth not perish, by the living word of God, who abideth for ever. (aiōn )
Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn )
but the word of our God abideth for ever: and this is the word that is announced to you. (aiōn )
amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn )
Whoever will speak, let him speak as the word of God: and whoever will minister, as of the ability that God hath given him: so that in all ye do, God may be glorified, through Jesus the Messiah; to whom belongeth glory, and honor, for ever and ever. Amen. (aiōn )
In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
Now it is the God of grace, who hath called us to his eternal glory by Jesus the Messiah, that hath given us, while we sustain these light afflictions, to be strengthened, and confirmed, and established by him for ever: (aiōnios )
Allah mai dukan alheri, wanda ya kira ku ga madawwamiyar ɗaukaka cikin Kiristi, bayan kun sha wahala na ɗan lokaci, shi da kansa zai raya ku, yă kuma sa ku yi ƙarfi, ku kahu, ku kuma tsaya daram. (aiōnios )
to whom be glory, and power, and honor, for ever and ever. Amen. (aiōn )
Gare shi bari iko yă tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
For thus will entrance be given you abundantly, into the everlasting kingdom of our Lord and Redeemer Jesus the Messiah. (aiōnios )
za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
For, if God spared not the angels that sinned, but cast them down to the infernal regions in chains of darkness, and delivered them up to be kept unto the judgment of torture, (Tartaroō )
Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
But be ye growing in grace, and in the knowledge of our Lord and Redeemer Jesus the Messiah, and of God the Father: whose is the glory, now, and always, and to the days of eternity. Amen. (aiōn )
Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn )
And the life was manifested, and we have seen and do testify and announce to you, the life which is eternal; which was with the Father, and was revealed to us. (aiōnios )
Wannan Rai ya bayyana, muka kuwa gan shi, muka kuma shaida shi, muna kuwa yin muku shelar wannan rai madawwami, wanda dā yake tare da Uba, ya kuma bayyana a gare mu. (aiōnios )
And the world is passing away, both it and the lust thereof; but he that doeth the pleasure of God, abideth for ever. (aiōn )
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
And this is the promise, which he hath promised us, even life eternal. (aiōnios )
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
For every one that hateth his brother, is a man-slayer; and ye know, that no man-slayer can have eternal life abiding in him. (aiōnios )
Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
And this is the testimony, that God hath given to us life eternal, and this life is in his Son. (aiōnios )
Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios )
These things have I written to you, that ye may know that ye have life eternal, ye who believe in the name of the Son of God. (aiōnios )
Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios )
And we know that the Son of God hath come, and hath given us knowledge that we might know the True One; and that we might be in the True One, in his Son Jesus the Messiah. He is the true God, and the life eternal. (aiōnios )
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios )
for the sake of the truth, which abideth in us and is with us for ever. (aiōn )
Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn )
And the angels that kept not their primacy, but left their station, he hath reserved in chains unknown, under darkness, unto the judgment of the great day. (aïdios )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
As Sodom and Gomorrah, and the surrounding cities, which in like manner followed whoredom and went after strange flesh, are placed beneath everlasting fire, being, doomed to judgment. (aiōnios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
raging waves of the sea, which, by their foam, manifest their confusion; shootingstars, for which is reserved the blackness of darkness for ever. (aiōn )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
And let us keep ourselves in the love of God, while we wait for the mercy of our Lord Jesus the Messiah unto our eternal life. (aiōnios )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
before his majesty, with joy, namely, the only God, our Deliverer, by means of Jesus the Messiah our Lord, be praise, and dominion, and honor, and majesty, both now and in all ages. Amen. (aiōn )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )
and hath made us a kingdom sacerdotal to God and his Father: to whom be glory and power, for ever and ever. Amen. (aiōn )
ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn )
and who liveth and was dead; and behold, I am alive for ever and ever. Amen. And I have the keys of death and of the unseen world. (aiōn , Hadēs )
Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn , Hadēs )
And when these Animals give glory and honor and praise to him that sitteth on the throne, to him who liveth for ever and ever, (aiōn )
Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn )
the twenty and four Elders fall down before him who sitteth on the throne, and they worship him who liveth for ever and ever; and they cast their coronets before the throne, saying, (aiōn )
sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn )
and to be over every created thing, that is in heaven, or on earth, or under the earth, or in the sea; and all that are in them. And I heard him who sat on the throne say: Unto the Lamb be given, blessing, and honor, and glory, and power, for ever and ever. (aiōn )
Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn )
And I looked, and lo, a pale horse; and the name of him who sat thereon was Death; and Hades followed after him. And there was given him authority over the fourth part of the earth, to slay with the sword, and by famine, and by death, and by the ravenous beast of the earth. (Hadēs )
Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya. (Hadēs )
saying: Amen. Blessing, and glory, and wisdom, and thanksgiving, and honor, and power, and might, be to our God, for ever and ever: Amen. (aiōn )
suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn )
And the fifth angel sounded; and I saw a star, which fell from heaven upon the earth. And there was given to him the key of the pit of the abyss. (Abyssos )
Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos )
And he opened the pit of the abyss; and smoke issued from the pit, like the smoke of a furnace that is in blast; and the sun and the air were darkened by the smoke of the pit. (Abyssos )
Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos )
And they had a king over them, the angel of the abyss; and his name, in Hebrew, is Abaddon; and in Greek, his name is Apollyon. (Abyssos )
Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos )
and swore, by him who liveth for ever and ever, who created heaven and the things in it, and the earth and the things in it, and the sea and the things in it, that the time should be no longer; (aiōn )
Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn )
And when they shall have completed their testimony, the beast of prey that came up from the abyss, will make war upon them, and will overcome them. (Abyssos )
To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos )
And the seventh angel sounded; and there were voices and thunders, which said: The kingdom of the world hath become the kingdom of our Lord and of his Messiah; and he will reign for ever and ever. (aiōn )
Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn )
And I saw another angel flying in heaven: and with blood, he had the everlasting gospel, to proclaim to dwellers on the earth, and to every nation and tribe and tongue and people; (aiōnios )
Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios )
And the smoke of their torment ascendeth up for ever and ever; and there is no rest, by day or by night, to those that worship the beast of prey and its image. (aiōn )
Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn )
And one of the four Animals gave to those seven angels seven cups of gold, full of the wrath of God who liveth for ever and ever. (aiōn )
Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn )
The beast of prey which thou sawest, was, and is not; and he will ascend from the abyss and go into perdition: and the dwellers on the earth, whose names are not written in the book of life from the foundation of the world, will wonder when they see the beast of prey, which was, and is not, and approacheth. (Abyssos )
Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos )
And again they said: Hallelujah: and her smoke ascendeth up for ever and ever. (aiōn )
Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn )
And the beast of prey was captured, and the false prophet that was with him, who did those prodigies before him, whereby he seduced them who had received the mark of the beast of prey and who worshipped his image. And they were both cast alive into the lake of fire, which burneth with sulphur. (Limnē Pyr )
Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr )
And I saw an angel that descended from heaven, having the key of the abyss, and a great chain in his hand. (Abyssos )
Na kuma ga wani mala’ika yana saukowa daga sama, yana da mabuɗin Abis yana kuma riƙe da ƙaton sarƙa a hannunsa. (Abyssos )
And he cast him into the abyss, and closed and sealed upon him; so that he might deceive the nations no more, until these thousand years shall be completed: but after that, he will be loosed for a little time. (Abyssos )
Ya jefa shi cikin Abis, ya kuma kulle ya sa hatimi a kansa, don a hana kada yă ƙara ruɗin al’ummai, sai shekarun nan dubu sun cika. Bayan wannan, dole a sake shi na ɗan lokaci. (Abyssos )
And the Accuser who seduced them, was cast into the lake of fire and sulphur, where also were the beast of prey and the false prophet: and they shall be tormented, day and night, for ever and ever. (aiōn , Limnē Pyr )
Aka jefa Iblis da ya ruɗe su cikin tafkin farar wuta, inda aka jefa dabban nan da annabin ƙaryan nan. Za a ba su azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn , Limnē Pyr )
And the sea gave up the dead in it; and death and the grave gave up the dead in them. And they were judged, each one according to his deeds. (Hadēs )
Teku ya ba da matattu da suke cikinsa, mutuwa da Hades kuma suka ba da matattu da suke cikinsu, aka kuma yi wa kowane mutum shari’a bisa ga abin da ya aikata. (Hadēs )
And death and the grave were cast into the lake of fire. This is the second death, namely, this lake of fire. (Hadēs , Limnē Pyr )
Sa’an nan aka jefar da mutuwa da kuma Hades cikin tafkin wuta. Tafkin wutar nan kuwa shi ne mutuwa ta biyu. (Hadēs , Limnē Pyr )
And if any one was not found enrolled in the book of life, he was cast into this lake of fire. (Limnē Pyr )
Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a cikin littafin rai ba, an jefar da shi cikin tafkin wutar nan. (Limnē Pyr )
But to the timid, and the unbelieving, and to the sinful, and polluted, and to manslayers, and whoremongers, and sorcerers, and idolaters, and to all false persons, their portion shall be in the lake that burneth with fire and sulphur, which is the second death. (Limnē Pyr )
Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.” (Limnē Pyr )
And there will be no more night; and they have no need of the light of a candle, or of the light of the sun; because the Lord God giveth them light: and they will reign for ever and ever. (aiōn )
Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )