< Revelation 22 +
1 And he showed me a river of living water, transparent as crystal, which proceeded from the throne of God and the Lamb.
Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
2 And in the middle of its broad avenue, and near the river, on this side and on that, was the tree of life; which bore twelve sorts of fruits yielding one of its fruits each month: and the leaves of the tree were for the healing of the nations.
yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
3 And there will be no blight any more: and the throne of God and the Lamb will be in it; and his servants will minister to him.
Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
4 And they will see his face, and his name will be on their foreheads.
Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
5 And there will be no more night; and they have no need of the light of a candle, or of the light of the sun; because the Lord God giveth them light: and they will reign for ever and ever. (aiōn )
Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
6 And he said to me: These words are faithful and true. And the Lord God of the spirit of the prophets, hath sent me, his angel, to show unto his servants the things that must soon occur.
Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
7 And, lo, I come quickly: Blessed is he that keepeth the words of the prophecy of this book.
“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
8 And more-over I am John, the hearer and the seer of these things. And when I heard and saw, I fell down to worship at the feet of the angel who showed me these things.
Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
9 And he said to me: See, thou do it not: I am thy fellow-servant, and of thy brethren the prophets, and of them that observe the words of this book. Worship God.
Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
10 And he said to me: Seal not the words of the prophecy of this book; for the time is near.
Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
11 He that doth evil, let him do evil still; and he that is filthy, let him be filthy still; and he that is righteous, let him practise righteousness still; and he that is sanctified, let him be sanctified still.
Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
12 Behold, I come quickly; and my reward is with me, to recompense every one according to his work.
“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
13 I am Alpha and Omega, the First and the Last, the Commencement and the Completion.
Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
14 Blessed are they who do his commandments, that they may have a right to the tree of life, and may enter through the gates into the city.
“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
15 Without will be dogs, and sorcerers, and whoremongers, and manslayers, and idolaters, and every one that loveth and doeth falsehood.
Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
16 I Jesus have sent my angel, to testify to you these things before the churches. I am the root and offspring of David: like the splendid star of the morning.
“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
17 And the Spirit and the bride say, Come thou. And let him that heareth, say, Come thou. And let him who thirsteth, come; and he that is inclined, let him take the living water gratis.
Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
18 I testify to every one that heareth the words of the prophecy of this book, that if any one shall add to them, God will add to him the plagues that are written in this book.
Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
19 And if any one shall take away from the words of the book of this prophecy, God will take away his portion from the tree of life, and from the holy city, which are described in this book.
Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
20 He who testifieth these things, saith: Yes, I come quickly. Amen. Come, Lord Jesus!
Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
21 The grace of our Lord Jesus the Messiah, be with all the saints. Amen.
Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.