< Romans 1 >

1 PAUL, a servant of Jesus the Messiah, called and sent; and separated unto the gospel of God,
Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
2 (which he had before promised, by his prophets, in the holy scriptures,
Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
3 concerning his Son, (who was born in the flesh, of seed of the house of David,
game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
4 and was made known as the Son of God, by power, and by the Holy Spirit, ) who arose from the dead, Jesus Messiah, our Lord,
Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
5 by whom we have received grace, and a mission among all the Gentiles, to the end that they may obey the faith in his name;
Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
6 among whom, ye also are called by Jesus Messiah; )
Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
7 to all those who are at Rome, beloved of God, called and sanctified: Peace and grace be with you, from God our Father, and from our Lord Jesus Messiah.
Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
8 In the first place, I give thanks to God by Jesus Messiah, on account of you all; because your faith is heard of in all the world.
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9 And God, whom in spirit I serve in the gospel of his Son, is my witness, that I unceasingly make mention of you, at all times, in my prayers.
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10 And I likewise supplicate, that hereafter a door may be opened to me, by the good pleasure of God, to come unto you.
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11 For I long much to see you; and to impart to you the gift of the Spirit, whereby ye may be established;
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12 and that we may have comfort together, in the faith of both yourselves and me.
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
13 And I wish you to know, my brethren, that I have many times desired to come to you, (though prevented hitherto, ) that I might have some fruit among you also; even as among other Gentiles,
Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
14 Greeks and barbarians, the wise and the unwise: for to every man am I a debtor, to preach to him.
Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
15 And so I am eager to preach to you also who are at Rome.
Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
16 For I am not ashamed of the gospel; for it is the power of God unto life, to all who believe in it; whether first they are of the Jews, or whether they are of the Gentiles.
Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
17 For in it is revealed the righteousness of God, from faith to faith; as it is written, The righteous by faith, shall live.
Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
18 For the wrath of God from heaven is revealed against all the iniquity and wickedness of men, who hold the truth in iniquity.
Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
19 Because a knowledge of God is manifest in them; for God hath manifested it in them.
gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
20 For, from the foundations of the world, the occult things of God are seen, by the intellect, in the things he created, even his eternal power and divinity; so that they might be without excuse; (aïdios g126)
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
21 because they knew God, and did not glorify him and give thanks to him as God, but became vain in their imaginings, and their unwise heart was darkened.
Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
22 And, while they thought within themselves that they were wise, they became fools.
Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
23 And they changed the glory of the incorruptible God into a likeness to the image of a corruptible man, and into the likeness of birds and quadrupeds and reptiles on the earth.
suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
24 For this cause, God gave them up to the filthy lusts of their heart, to dishonor their bodies with them.
Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
25 And they changed the truth of God into a lie; and worshipped and served the created things, much more than the Creator of them, to whom belong glory and blessing, for ever and ever: Amen. (aiōn g165)
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 For this cause, God gave them up to vile passions: for their females changed the use of their natures, and employed that which is unnatural.
Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
27 And so also their males forsook the use of females, which is natural, and burned with lust toward one another; and, male with male, they did what is shameful, and received in themselves the just recompense of their error.
Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
28 And as they did not determine with themselves to know God, God gave them over to a vain mind; that they might do what they ought not,
Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
29 being full of all iniquity, and lewdness, and bitterness, and malice, and covetousness, and envy, and slaughter, and strife, and guile, and evil machinations,
Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
30 and backbiting, and slander; and being haters of God, scoffers, proud, vain-glorious, devisers of evil things, destitute of reason, disregardful of parents,
da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
31 and to whom a covenant is nothing, neither affection, nor peace, and in whom is no compassion.
su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
32 These, while they know the judgment of God, that he condemneth those to death who perpetrate such things, are not only doers of them, but the companions of such as do them.
Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.

< Romans 1 >