< John 13 >
1 Now before the feast of the Passover, Jesus, having seen that his hour has come that he would depart out of this world to his Father, having loved his own in the world, he loved them to the end.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 And supper having occurred, the devil having now put into the heart of Judas Iscariot, Simon's son, that he would betray him,
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 Jesus, having seen that the Father has given all the things to him, into his hands, and that he came from God, and goes to God,
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 rises from supper, and set his garments aside, and after taking a towel, he girded himself.
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Then he pours water into the wash-basin, and began to wash the disciples' feet, and to wipe them with the towel with which he was girded.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 So he comes to Simon Peter, and that man says to him, Lord, do thou wash my feet?
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 Jesus answered and said to him, What I do thou do not know now, but thou will understand after these things.
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 Peter says to him, Thou may, no, not wash my feet into the age. Jesus answered him, If I may not wash thee, thou have no part with me. (aiōn )
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
9 Simon Peter says to him, Lord, not my feet only, but also my hands and head.
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 Jesus says to him, He who is bathed has no need to wash the feet either, but is entirely clean. And ye are clean, but not all.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 For he knew the man betraying him. Because of this he said, Ye are not all clean.
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 When therefore he washed their feet, and took his garments, having sat down again, he said to them, Do ye understand what I have done to you?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 Ye call me, Teacher, and, Lord. And ye say well, for I am.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 If I then, the Lord and the teacher, have washed your feet, ye also ought to wash each other's feet.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 For I have given you an example, so that just as I have done to you ye also should do.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 Truly, truly, I say to you, a bondman is not greater than his lord, nor is an apostle greater than he who sent him.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 If ye have seen these things, blessed are ye if ye do them.
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 I speak not about you all. I have seen whom I chose, but that the scripture may be fulfilled, He who eats bread with me lifted up his heel against me.
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 From henceforth I tell you before it happens, so that when it happens, ye may believe that I am.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Truly, truly, I say to you, he who receives any man whomever I may send, receives me, and he who receives me receives him who sent me.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 Having said these things, Jesus was troubled in the spirit, and testified and said, Truly, truly, I say to you, that one of you will betray me.
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Therefore the disciples looked at each other, being uncertain about whom he speaks.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 And one of his disciples whom Jesus loved was sitting at Jesus' bosom.
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 Simon Peter therefore gestured to this man to inquire whoever he may be about whom he speaks.
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 And that man, having leaned thus toward Jesus' breast, says to him, Lord, who is he?
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 Jesus replies, He is that man to whom I, having dipped the morsel, will give. And when he dipped the morsel, he gives it to Judas Iscariot, the son of Simon.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 And after the morsel, then Satan entered into that man. Jesus therefore says to him, What thou do, do more quickly.
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 But no man who was sitting knew why he said this to him.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 For some thought, since Judas had the purse, that Jesus said to him, Buy what things we have need of for the feast, or that he should give something to the poor.
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 Therefore having received the morsel, straightaway that man went out, and it was night.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 When he went out, Jesus says, Now the Son of man is glorified, and God is glorified in him.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 If God is glorify in him, God will also glorify him in himself, and he will glorify him straightaway.
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 Little children, yet a little while I am with you. Ye will seek me, and as I said to the Jews, Where I go, ye cannot come, I also now say to you.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 A new commandment I give to you, that ye should love each other, just as I loved you, so that ye also should love each other.
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 By this all men will know that ye are my disciples, if ye have love among each other.
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 Simon Peter says to him, Lord, where do thou go? Jesus answered him, Where I go, thou cannot follow me now, but thou will follow me afterwards.
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 Peter said to him, Lord, why cannot I follow thee now? I will lay down my life for thee.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 Jesus answered him, Will thou lay down thy life for me? Truly, truly, I say to thee, A cock will, no, not sound, until thou will deny me thrice.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!