< John 11 >

1 Now a certain Lazarus, from Bethany of the village of Mary and her sister Martha, was sick.
To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
2 And Mary was the woman who anointed the Lord with ointment, and wiped his feet with her hair, whose brother Lazarus was sick.
Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
3 The sisters therefore sent to him, saying, Lord, behold, he whom thou love is sick.
Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
4 But when Jesus heard, he said, This sickness is not about death, but for the glory of God, so that the Son of God may be glorified by it.
Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
5 Now Jesus loved Martha and her sister and Lazarus.
Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
6 When therefore he heard that he is sick, then he actually remained two days in that place he was.
Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
7 Later after this he says to the disciples, Let us go into Judea again.
Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
8 The disciples say to him, Rabbi, the Jews were now seeking to stone thee, and thou go there again.
Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
9 Jesus answered, Are there not twelve hours in the day? If a man walks in the day, he does not stumble, because he sees the light of this world.
Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
10 But if any man walks in the night, he stumbles, because the light is not in him.
Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
11 He spoke these things, and after this he says to them, Our friend Lazarus has become asleep, but I go that I may awake him.
Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
12 His disciples therefore said, Lord, if he has become asleep, he will be healed.
Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
13 But Jesus had spoken about his death, but those men thought that he was speaking about the restfulness of sleep.
Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
14 Therefore Jesus then said to them plainly, Lazarus died.
Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
15 And I am glad for your sakes that I was not there, so that ye may believe. Nevertheless let us go to him.
amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
16 Therefore Thomas, called Didymus, said to his fellow disciples, Let us also go, that we may die with him.
Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
17 So when Jesus came, he found him already four days being kept in the sepulcher.
Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
18 Now Bethany was near Jerusalem, about fifteen furlongs away from it,
Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
19 and many of the Jews had come to the women, about Martha and Mary, so that they might console them about their brother.
Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
20 Therefore Martha, when she heard that Jesus was coming, met him, but Mary was sitting in the house.
Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
21 Martha therefore said to Jesus, Lord, if thou were here, my brother would not have died.
Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
22 But I know even now that as many things as thou may ask of God, God will give to thee.
Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
23 Jesus says to her, Thy brother will rise.
Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
24 Martha says to him, I know that he will rise in the resurrection at the last day.
Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
25 Jesus said to her, I am the resurrection and the life. He who believes in me, even though he died, he will live.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
26 And every man who lives and believes in me will, no, not die, into the age. Do thou believe this? (aiōn g165)
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
27 She says to him, Yes, Lord, I have believed that thou are the Christ, the Son of God who comes into the world.
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
28 And when she said these things, she departed and called Mary her sister privately, saying, The teacher is here and calls thee.
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
29 When that woman heard, she rises quickly, and comes to him.
Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
30 (Now Jesus had not yet come into the village, but was in the place where Martha met him.)
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
31 The Jews therefore being with her in the house and consoling her, having seen Mary, that she rose up quickly and went out, followed her, saying that she was going to the sepulcher that she may weep there.
Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
32 Therefore when Mary came where Jesus was, after seeing him, she fell down at his feet, saying to him, Lord, if thou were here, my brother would not have died.
Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
33 When Jesus therefore saw her weeping, and the Jews who gathered with her, weeping, he groaned in the spirit, and was himself troubled.
Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
34 And he said, Where have ye laid him? They said to him, Lord, come and see.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
35 Jesus wept.
Yesu ya yi kuka.
36 The Jews therefore said, Behold how he loved him.
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
37 But some of them said, This man who opened the eyes of the blind man, was he not also able to cause that this man also would not die?
Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
38 Jesus therefore again groaning in himself comes to the sepulcher. Now it was a cave, and a stone lay against it.
Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
39 Jesus says, Take ye away the stone. Martha, the sister of the man who came to end, says to him, Lord, he smells now, for it is the fourth day.
Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
40 Jesus says to her, Did I not to say thee, that if thou believed, thou will see the glory of God?
Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
41 So they took away the stone where the man who died was laying. And Jesus lifted up his eyes, and said, Father, I thank thee that thou heard me.
Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
42 And I had known that thou always hear me, but because of the multitude that stands by I spoke, so that they may believe that thou sent me.
Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
43 And having said these things, he cried out with a great voice, Lazarus, come out.
Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
44 And the man who died came forth, wrapped hands and feet with grave-clothes, and his face had been wrapped around with a face cloth. Jesus says to them, Loose him, and allow him to go.
Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
45 Therefore many of the Jews who came to Mary, and who saw what Jesus did, believed in him.
Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
46 But some of them went away to the Pharisees, and told them what things Jesus did.
Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
47 Therefore the chief priests and the Pharisees gathered a council, and said, What are we doing? Because this man does many signs.
Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
48 If we allow him this way, all men will believe in him, and the Romans will come and take away both our place and the nation.
In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
49 And a certain one of them, Caiaphas, being high priest that year, said to them, Ye know nothing at all,
Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
50 nor do ye consider that it is expedient for us that one man should die for the people, and not the whole nation should perish.
Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
51 Now he said this not from himself, but being high priest that year, he prophesied that Jesus was going to die for the nation.
Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
52 And not for the nation only, but also that he might gather together into one the children of God who are scattered abroad.
ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
53 So from that day they consulted together so that they might kill him.
Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
54 Jesus therefore no longer walked openly among the Jews, but departed from there into the region near the wilderness into a city called Ephraim, and he stayed there with his disciples.
Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
55 Now the Passover of the Jews was near, and many went up to Jerusalem out of the countryside before the Passover, so that they might purify themselves.
Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
56 Therefore they sought Jesus, and spoke with each other as they stood in the temple, What does it seem to you? That he will, no, not come to the feast?
Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
57 Now also the chief priests and the Pharisees had given commandment, that if any man knew where he is, he should disclose it, so that they might take him.
Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.

< John 11 >