< Acts 1 >
1 I indeed made the former treatise, O Theophilus, about all things that Jesus began both to do and to teach,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 until a day in which he was taken up, having commanded, through the Holy Spirit, the apostles whom he chose,
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 to whom he also presented himself living, after his suffering, by many infallible proofs, being seen by them during forty days, and speaking the things about the kingdom of God.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 And being assembled together, he commanded them not to depart from Jerusalem, but to wait for the promise of the Father, Which, he said, ye heard from me.
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 Because John indeed immersed in water, but ye will be immersed in the Holy Spirit after not many of these days.
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 Indeed therefore having come together, they questioned him, saying, Lord, do thou restore the kingdom to Israel at this time?
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 And he said to them, It is not for you to know times or seasons, which the Father established in his own authority.
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 But ye will receive the power of the Holy Spirit that comes upon you. And ye will be witnesses to me both in Jerusalem, and in all Judea and Samaria, and as far as of the extremity of the earth.
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 And having said these things, as they were watching, he was taken up, and a cloud received him from their eyes.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 And while they were gazing at his going into the sky, behold, two men had also stood by them in white apparel,
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 who also said, Men, Galileans, why stand ye gazing into the sky? This Jesus who was taken up from you into the sky will so come, in that same way as ye saw him going into the sky.
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Then they returned to Jerusalem from the mountain called Olivet, which is near Jerusalem having a sabbath day journey.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 And when they came in, they went up into the upper floor where they were lodging, including, Peter and James and John and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew and Matthew, James the son of Alphaeus, and Simon the Zealot, and Judas son of James.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 All these men were continuing with one accord in prayer and supplication, with women, and Mary the mother of Jesus, and with his brothers.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 And in those days, Peter, having stood up in the midst of the disciples (and there was a multitude of names at the same place, about a hundred twenty), he said,
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 Men, brothers, it was necessary for this scripture to be fulfilled, which the Holy Spirit foretold through the mouth of David about Judas, who became a guide to those who arrested Jesus,
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 because he was numbered with us, and received a share of this ministry.
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 (Indeed therefore this man obtained a field from the reward of his unrighteousness, and having become headlong, he burst open in the middle and all his bowels gushed out.
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 And it became known to all those dwelling at Jerusalem, so as to call that field in their own dialect, Akeldama, that is, The field of blood.)
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 For it is written in the book of Psalms, Let his habitation become desolate, and let no man be dwelling in it, and, Let another take his office.
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 It is necessary therefore, of the men who accompanied us during all the time during which the Lord Jesus went in and went out among us,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 having begun from the immersion of John to the day that he was taken up from us, for one of these to become a witness with us of his resurrection.
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 And they put forward two, Joseph called Barsabbas, who was surnamed Justus, and Matthias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 And having prayed, they said, Thou, Lord, knowing the hearts of all men, show which one of these two thou have chosen
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 to take the place in this ministry and apostleship from which Judas transgressed to go to his own place.
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 And they gave their lots, and the lot fell upon Matthias, and he was numbered with the eleven apostles.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.