< Mark 16 >

1 niwa i vi u asabarchi a wuce Maryamu ba magadaliya mba salome ba ka nji izyi kpa ye nde ba gban ni yesu nikpa
Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
2 ni bwubwu ble ni vi mule u satia u ba hi ni beh ni nza hongan
A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
3 u ba myen kpamba a di a nhan ni nyiu tita rju ni tawu ni yiu beh hia?
sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
4 u ba nzu shishi ya na toh ba nyiu tita rju ye tita a ki kle ma gbenme
Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
5 u ba luri ni mi na toh vren nze ri sur nklo kinkle son ni wo kori uba bwu yiu
Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
6 wa hla ni bawu na bwu yiu na bi si wa yesu ba nazaraten wa ba giciye niwu alude n a na hei na ya ige bubu wa ba kah yo yi
Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
7 ama bika hi kpambi ni ha ni almajere ma nie Bitrus a hei koshishi si hi ni galilis ni mun bi toh nawa a hla ni yiua
Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
8 u ba dorju ni mi beh ni wi likpa ni bwuyiu bana ya tre kpieri me ni kpambana nitu sisir
Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) nta shime ni bwumble ni vi u mumlan u satia da guchi ye rju ni mary magadaliya na ju meme ibrji tar gban rju niwu
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
10 wa hi na kah bla nibi wa ba hei ni wua da katsira ba si ta mre da ni yi
Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
11 i ba wo da hei ni rei u wawu toh ni shishima ama u bana kpa nyeme na
Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
12 wa rju ni babwu ha mba ni kon rimu kan yada ba rju nigbua zren sihi kpamba
Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
14 ni ko ngo ki yesu lu rju ni wolon don ri uba si rila ni tu tebru wa pwa ba tre nitu wa bana kpanyemena da nsei tu da na kpanyemen ni biwa da toh shishi nishishi na hla ba hi wu a ndi alude na
Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
15 a hla bawu ndu ba hi na hla tre ma ni ndi bi rgbungbulu ba kagon wawusu
Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
16 indi wa a kpa nyeme na ndu ba yi batisma niwua ani nawo indi wa ana kpa nyemen na ani rilu
Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
17 ba toh tie bi yii ni biwa ba kpatre rji ba zu brji ni nde mu ba tre lme sama
Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
18 ba ya vuwam ni wo ana tie ba kpie na ko ba so meme gbugbulu ana tie ba kpie na
Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
19 yesu tre kle ni ba wu uba ban hi ni shulu waka son ni wo ko ri irji
Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
20 u baluri blatre rji kango gbungbulu a irji ni zo ba na kpanyeme ni tre mba nikpii wa a tre ba tie baa
Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.

< Mark 16 >