+ Matiyu 1 >
1 Vuvu u Yesu Kristi ivren Dauda, ivren u Ibrahim.
Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
2 Ibrahim a ngrji Ishaku, Ishaku ka ngrji Yakubu, u Yakubu a ngrji Yahuda ni ba mrli vayi ma.
Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
3 Yahuda a ngrji Perez mba Zerah ngrji u Tamar, Perez ngrji Hezron, u Hezron ngrji Ram.
Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
4 Ram ngrji Amminadah, Amminadah ngrji Nahshon, u Nahshon ngrji Salmon.
Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
5 Salmon ngrji Boaz ngrji Rahab, Baoz ngrji Obadiya ngrji u Rautha, Obadiya ngrji Jesse.
Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
6 U Jesse ngrji ichu Dauda. Ichu Dauda ngrji Suleman wa iyima ana wa Uraya
Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
7 Suleman a nu ngrji Rehoboam, Rehoboam a ngrji Abijah u Abijah ngrji Asa.
Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
8 Asa ngrji Jehoshafat, Jehoshafat ngrji Joram, Joram ngrji Uzziya.
Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
9 Uzziya ngrji Jotham, Jotham ngrji Ahaz u Ahaz ngrji Hezekaya.
Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
10 Hazekaya a ngrji Manaseh, Manaseh a ngrji Amon u Amon ngrji Yosiya.
Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
11 Yosiya ngrji Yekoniya ni mrli vayi ma wiere me ni nton wa ba vu ba hi ni Babila.
Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
12 U wa ba nji ye Babila, Yekoniya ngrji Shealtiel u Shealtiel ngrji Yerubabel.
Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
13 Yerubabel ngrji Abuid, Abuid ngrji Eliakim, u Eliakim ngrji Azor.
Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
14 Azor ngrji Zadok, Zadok ngrji Achim u Achim ngrji Eliud.
Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
15 Eliud ngrji Eleazer, Eleazer
Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
16 ngrji Matthan, u Matthan ngrji Yakubu. U Yakubu ngrji Yusufu illon Maryamu wa a ngrji Yesu wa ba yo'u din Kristi.
Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
17 To inzan ba wawu rji ni Ibrahim hi Dauda ba wlon don zia, rji ni Dauda hi ntton wa ba vu hi ni Babila bahi izan zia, u rji ni ni ntton u wa bahe ni Babila hi ni ye Kristi ba nzan wlon don zia.
Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
18 Ingrji Yesu Kristi ahe towa: wa ba nna yima Maryamu ni Yusufu gben ntton wa baka gran kpa, u nne Ruhu tsatsar ye riwu.
Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
19 U Yusufu illon ma indi u klu Rji, nda na son nno shan na, a cu sron ma rju ni gran nda kama ni wu niyay'bi (aboye)
Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
20 Amma, asi tamre towa, u malaika Baci ka ye niwu ni rah nda tre, “Yusufu, ivren Dauda, na klu sisri ban wame Maryamu na, don ikpie a wrji anne ma, a u Ruhu tsatsar.
Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
21 Ani ngrji vrenlon wa u yowu ndi Yesu, don ani kpa ndi ma cuwo ni gbugbu latre mba.
Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 To, ahe to yi don ndu tre Baci he na wa a hla din.
Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
23 “To mba, vivren wa ri wa ana to lillona ani ye he nne nda ngrji vrenlon wa ba yo wa ndi Imanuwal” wa hi riri ni “Irji he nita”
“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
24 U Yusufu, gbla sh'me ni nah tie ikpie wa Malaika hla niwu nda hi ka ban wa-a hi ni kpama.
Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
25 Ana rlihe toh wa-a sai wa a ngrji vren ma u mumla. Ayo nde ma di Yesu.
Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.