< Mark 15 >
1 ni bwu ble frist bi nikon ba shubi ni bi nikon gbua u bi nha u tra rji ni yahudawa wa babi suronmua ba vu yesu lo nda njiu nda hi ba kau nno Bilatus
Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
2 Bilatus myeu awu yi u ehu Yahudawa? a sa ni wu andi u tre toki
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
3 frist bi nikon ba nhau ni kpi gbugbu wu
Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
4 Bilatus a la mye u na hla na ka nche? to gbugbu tre wa ba ki nha wu ni tu mba
Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
5 yesu ana la sa ni Bilatus ngana wa anno mamaki
Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
6 to ni ntto u gan Bilatus a ta chi ndi bi la tre ri wa he troa chuwa indi wa ba kabre ni tu ma
Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
7 u igu ni mbru bi la tre ba latre u wu ndi
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
8 ijubu ndi ba ye niye Bilatus ndu tie ikpie waazi tie rji mu
Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
9 Bilatus ka sa bawu bi nyem ndu me kah chu yahudawa chuwo?
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
10 a to nda ni tu ngu mba baka vu yesu njiwu
Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
11 amma nji frist ba ba con jbu ndi ba ndu ba yar gro ndu ba ka Barabbas mba cuwo
Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
12 Bilatus a la mye mba ngarli a hi ngye mba tie ni chu Yahudawa?
Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
14 Bilatus mye ba a latre ngye a tie? u ba tutu yar gre clou
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
15 Bilatus a son tie kpie a ba wa nda ka Barabbas cuwo ni ba wu a pua yesu tre rli nda kau nno ba kpa klo
Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
16 soja ba bu nji nda hi ni tra u bla tre nda u yo soja ba wawuu kabi
Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
17 ba lo tuma ni pli u ma klo ntme wiwrli nda con con lo nha
Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
18 ba wlu nda ciu ndatre ndu rji ziu iclu yahudawa
Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
19 ba grji tsiu ni tu ni gbugban u con ma nda ju nte ta sur ba kuqu gbarju nda kudran ni kbu ma
Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
20 sa ba chauya ba chu pii u tuma rju hi ni wrji wa ba hi kpam wua
Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
21 indi ri siman u gbu siren sia ye rji gburi ba vu ni gbengble to ban kukron krossa
Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
22 soja ba nji yesu hi ni wrji wa ba yo ndi golgota
Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
23 ba nno ma kabi ba mur wa a kama nda na soh na
Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
24 ba kpan wu nda vu klon ma rli nra ni kpa mba
Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
25 ba kpan u ni tu kukron ni ntton u tra
Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
26 ba nha ni ple kukron ni ikpie a ba nhaua ichu yaluda
Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
27 ba kpanwu ni bi ybi harli iri ni wo rli u ri ni wo kota
Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
28 i wa yi ye tsar ni tre rji wa a hla ba bla kabi ni bi latre
29 biwa ba ka ki hia ba zren da ni whu tu nda ni tre yowa iwuwa u zii tra rji ni meu ni mi vi tra nra kpame ndi grji ni kakrona
Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
30 nji frist ni bi nha ba ba chauyaya ngame ni kpa mba da tre
sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
31 a ndi a kpa bai cuwo amma nda na to kpa kpama cuwo na
Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
32 ndu kristi ichu israilawa ba grji ni gran kukron a ye meme zizanyi ndu ki to ndi kpa nyme ni wu bi wa ba kpan ba ni yesu ba hlo tre ni me
Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
33 ni ntton u tane ibwu ye kah gbu wawuu hi ni ntton u tia
Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
34 ni ntton u tia yesu ka yar yi gbagban me eloi eloi lama sabachthani? wa hi irji mu irji mu u tie he rli kame don?
A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
35 bi wa ba kli wi riha kia ba wo lan tre ma nda tre din to ba a si Iliya
Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
36 indi ri tsutsu ka yo rlikpanma ni ma waasa nda kason ni gbondo kpala nda kanno ndu soh igua tre din ki to ka Iliya ni ye njiu grji
Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
37 ni ki yesu ka yar yi gbangban me nda qu
Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
38 ipli u tra rjia ka yra tie harli rji ni tu mu grji hi kogboma
Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
39 da jirmi wa kli nda si ya yesu a to ndi yesu qu ye to wa a tre din njanjimu igu yi ana vren rji imba bari ngame baki gbigbanmu nda kia yah vimi mba ana ba maryamu ba mag daliya maryamu u salomi
Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
41 wa a he ni Galili ba hu nda ta tie ndu wu imba gbugbu u ngame ba huhi ni urshalima
A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
42 wa yalu tiea don he u mlaki ivi wa baka rjo ri ni sabath
Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
43 Yusufu indi u Arimathiya ye ni ki ana ri ri bi lo chu ndi wa bata nno grima nda sia gben mulki rji avu sran nda shi ni Bilatus nda mye kmo yesu
Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
44 Bilatus tie sisri ndi yesu qu ayo jirme a nda wo ka yesu qu
Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
45 da Bilatus a wo ni nyu jirmea ndi yesu qu ye a nno kmboa ni Yusufu
Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
46 Yusufu ana le plia ye a grji kumo ni grani kukrona nda lou ni pli nda nji he ka yo ni beh wa ana tita wa ba tsen mlatie a tru tita hra beh a ka nyu beha
Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
47 maryamu ba mag daliya ni Maryamu iyi yosi ba to bubu wa ba rju yesu
Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.