< 1 Wakoritho 7 >
1 Kusino mukandembile: ghamo masiki manofu umughosi nangaghonaghe nu n'dala ghwa mwene.
Game da abubuwan da kuka rubuto: “Yayi kyau ga mutum kada ya taba mace.”
2 Looli lino ulwakuva ingelo nyinga isavuvwafu umughosi ghwenu avisaghe nu muunhu ghwa mwene na ghweni un'dala avisaghe numughosi ghwa mwene.
Amma Saboda jarabobi na ayyukan fasikanci masu yawa, ya kamata kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma ta kasance da mijinta.
3 Umughosi anoghile pikum'pela umuunhu ghwa mwene luno lunoghile musavutolani vwa mwene, kange vulevule naju n'dala am'pelaghe luno lunoghile umughosi ghwamwene.
Kowanne maigidanci ya ba matarsa hakin ta, kuma kowace mace ta ba maigidan ta hakinsa na saduwa da juna.
4 Na ghwe n'dala juno alinuvutemi mum'biili ghwa mwene, ghwe mughosi. Kange vulevule najumughosi nalinnuvutemi vwa m'biili ghwa mwene, looli un'dala ghwa mwene ghwe alinavo
Matan ba ta da iko akan jikin ta amma maigidan ne. Haka ma, maigidan bashi da iko akan jikinsa amma matar ce.
5 Namungafinyanaghe pano mughona palikimo, looli nave mupuling'line kunsiki ghuno ghuvikilue. Muvombaghe vulevule ulwakuuti mukave nsiki ghwa kufunya. Kange lunoghile pigomokilanila palikimo, ulwakuuti usetano aleke kukuvaghela kukiling'ania kyongo.
Kada ku hana wa junanku saduwa, sai dai da yardar junanku domin wani dan lokaci. Kuyi haka domin ku bada kanku ga addu'a. Daganan sai ku sake saduwa, domin kada Shaidan ya jarabce ku saboda rashin kamun kanku.
6 Looli nijova ku isi soni nuvwavuke nakwekuuti lulaghilo.
Amma ina fada maku wadannan abubuwa ne a matsayin nuni, ba a matsayin umurni ba.
7 Ninoghelua umuunhu ghweni asava ndavule une nilivuo. Looli umuunhu ghweni alinikipelua kyamwene kuhuma kwa Nguluve. Uju alinikipelua iki, ghwope jula alinikipelua kila
Na so da kowa da kowa kamar ni yake. Amma kowa na da baiwarsa daga wurin Allah. Wani na da irin wannan baiwar, wani kuma waccan.
8 Kuvano navatolilue navafwile niiti ndiki, luvele luvanoghile vajighe kisila kutolua, ndavule nilivuo unhe.
Ga marasa aure da gwamraye, Ina cewa, yana da kyau a garesu su zauna ba aure, kamar yadda nike.
9 Looli nave pikusigha, luvanoghile pitolua. Ulwakuva luvanoghile avene kutolua ulwakuuti valeke kuva nuvunoghelua.
Amma idan baza su iya kame kansu ba, ya kamata su yi aure. Gama yafi masu kyau su yi aure da su kuna da sha'awa.
10 Lino kuvano vitolua nikuvapela ululaghilo, na nene ghwe Mutwa, “Umumama nangalekanaghe nu mughosi ghwa mwene.”
Ga masu aure kwa, ina bada wannan umarni- ba ni ba, amma Ubangiji: “Kada mace ta rabu da mijinta.”
11 Looli nave alekeng'ine kuhuma kwa mughosi, ajighaghe vulevule nangatoluaghe kange nambe lunoghile anoghile kupulingana kange numughosi ghwa mwene. Na “Jumughosi nangam'pelaghe italaka umuunhu ghwa mwene.”
Amma idan har ta rabu da mijinta, sai ta zauna ba aure ko kuma ta shirya da shi. Haka kuma “Kada miji ya saki matarsa.”
12 Looli kuvano vasighile, niiti- unhe, nakwekuuti u Mutwa- kuuti nde unyalukolo ghweni alinumuunhu ghwa mwene juno na ikwitika kange akwiline oikukala naghwope nanoghilele pikumuleka.
Amma ga sauran ina cewa-Ni, ba Ubangiji ba-idan wani dan'uwa yana da mata wadda ba mai bi ba, kuma idan ta yarda ta zauna da shi, to kada ya sake ta.
13 Nave umukimama naitike, nave akwiline kukukala naghwope nanga mulekaghe.
Idan kuwa mace tana da miji marar bi, idan ya yarda ya zauna tare da ita, to kada ta kashe aure da shi.
14 Kwa mughosi juno naitike ivalasivua vwimila vwa lwitiko lwa muunhu ghwa mwene. Na jumumama juno naitike ivalasivua vwimila vwa mughosi ghwa mwene juno itike. Nafyelusava avuo avanha viinhu vale vivanavanofu, looli kyang'haani vavalasivue.
Gama miji marar bada gaskiya ya zama kebabbe saboda matarsa, sannan mata marar bada gaskiya ta zama kebbiya saboda mijinta mai bi. In ba haka ba 'ya'yanku za su zama marasa tsarki, amma a zahiri su kebabbu ne.
15 Looli umughanike juno namwiti anagavuke alutaghe. Pa uluo, unkulu nambe umwanilumbu naikungua ni njiigho savanave. Unguluve atukemelile tukalaghe nhu lutengano.
Amma idan abokin aure marar bi ya fita, a bar shi ya tafi. A irin wannan hali, dan'uwa ko 'yar'uwa ba a daure suke ga alkawarinsu ba. Allah ya kira mu da mu zauna cikin salama.
16 Ukagula ndani nave ulin'dala pano ukum'pokagha umughosi ghwako? Nambe ghukagula ndani nave umughosi, nighani ghukum'poka umuunhu ghwako?
Yaya kika sani, ke mace, ko za ki ceci mijinki? ko yaya ka sani, kai miji, ko za ka ceci matarka?
17 Umuunhu ghweni ikalaghe ndavule u Mutwa avaghavile, umuunhu ghweni ndavule u Nguluve avakemelile avene. Uvu vwe vulongosi vwango ku ng'ong'ano sooni.
Bari dai kowa ya yi rayuwar da Ubangiji ya aiyana masa, kamar yadda Allah ya kirawo shi. Wannan ce ka'idata a dukkan ikilisiyu.
18 Pwale juno akadumulilue yeakemelilue mulwitiko? Alaghelagha kuvusia ikivalilo kya vudumulilua. Pwale jumonga juno akemelilue mu lwitiko nadumulilue? Nalunoghile kudumulua.
Mutum na da kaciya sa'adda aka kira shi ga bada gaskiya? Kada yayi kokarin bayyana kamar marar kaciya. Mutum ba shi da kaciya sa'adda aka kira ga bangaskiya? To kada ya bidi kaciya.
19 Pa uluo kuva adumulivue nambe juno nadumulivue kusita lumonga. Ikinyalumonga kwe kupulika indaghilo sa Nguluve.
Gama kaciya ko rashin kaciya ba shine mahimmin abu ba. Mahimmin abu shine biyayya da dokokin Allah.
20 Umuunhu ghweni asighalaghe mung'emelo ndavule alyale ye ikemelua nu Nguluve pano ikwitika.
Kowa ya tsaya cikin kiran da yake lokacin da Allah ya kira shi ga bada gaskiya.
21 Ulyale nkami unsiki ghuno u Nguluve ikukukemela? Nungasaghaghe ku uluo. looli nave ghuvaghila kuva mwavuke, vombagha vulevule.
Kai bawa ne lokacin da Allah ya kirawo ka? Kada ka damu da haka. Amma idan kana da zarafin samun 'yanci, ka yi haka.
22 Kwajumo juno juno akemelilue nhu Mutwa hene nkami muunhu mwavuke mwa Mutwa. Ndavule, viino jumo juno mwavuke kukwitika ghwe nkami ghwa Kilisite.
Domin wanda Ubangiji ya kira shi lokacin da yake bawa, shi 'yantacce ne na Ubangiji. Hakanan kuma, wanda shike 'yantacce lokacin da aka kira shi ga bada gaskiya, Bawan Almasihu ne.
23 Mumalile kughulua ni kyuma kinga, pa uluo mulekaghe piiva vakami va vaanhu.
An saye ku da tsada, donhaka kada ku zama bayin mutane.
24 Vakuulu numue va mwanilumbu vango, mu mikalile ghooni umuunhu ghweeni ndavule tulyakemelilue kukwitika, tujighaghe vulevule
Yan'uwa, a kowace irin rayuwa kowannenmu ke ciki lokacin da aka kira mu ga bada gaskiya, bari mu tsaya a haka.
25 Lino, vala voni vano navalile nambe, n'sila lulaghilo kuhuma kwa Mutwa. Looli nikuvapela imavilo sango ndavule nilivuo. Mulusungu lwa Mutwa luno lwa kyang'haani.
Game da wadanda basu taba aure ba, ba ni da wani umarni daga wurin Ubangiji. Amma ina bada ra'ayina kamar mutum wanda, ta wurin jinkan Allah, yake yardajje.
26 Looli, nisagha ndike ulwakuva sa lugasio, lunoghile umughosi ajighaghe ndavule alivuo.
Don haka, Ina ganin saboda yamutsin dake tafe ba da jimawa ba, ya yi kyau mutum ya zauna yadda yake.
27 Ukungilue kwa muunhu ghwako nulufingo lwa vutolani? Nungalondaghe uvwavuke kuhuma ku uluo. Ulimwavuke kuhuma kwa muunhu ghwako nakuva nutolilue? Nungamulondaghe umu mama.
Kana daure da mace? Kada ka nemi 'yanci daga gare ta. Baka daure da mace? Kada ka nemi auren mace.
28 Looli nave nutolilue, nuvombile amakole. Vasighile vala vano navatolano viva ni ngasio jino silipapinga. Une nilonda nivaseghusie ku isio.
Amma idan ka yi aure, ba ka yi zunubi ba. Kuma idan mace marar aure ta yi aure, bata yi zunubi ba. Saidai su wadanda suka yi aure za sha wahalhalu iri-iri a yayinda suke raye, kuma ina so in raba ku da su.
29 Looli nijova ndiiki, vakuulubnumue valumbu vango, un'siki n'debe. Kuhumalino na kughendelela vaala vano valinava mama vikalaghe hweene valivuvule.
Amma wannan nike fadi ya'nuwa: lokaci ya kure. Daga yanzu, bari wadanda suke da mata suyi rayuwa kamar basu da su.
30 Vooni vano vasasukunile vavisaghe hene vasila lusukunalo, vooni vano vakalile, nave navakakelile, na vooni vano vighula ikiinhu kyoni, nave navahalile kimonga.
Masu kuka su zama kamar marasa kuka, masu farinciki kamar marasa farinciki, masu sayen abubuwa kamar marasa komai.
31 Vooni vano vitigha ni iisi, vave heene navakale vitigha na veene, ulwakuuva amatindo gha iisighifikila uvusililo vwa mwene.
Wadanda suke harka da duniya kamar ba su harka da ita, domin ka'idar duniyan nan tana kawowa ga karshe.
32 Nilonda muve vavuke mu ngasio soni. umughosi juno natolile ivomba ifiinu fya Mutwa, ndavule inoghelua umwene.
Ina so ku kubuta daga damuwa mai yawa. Mutum marar aure yana tunani akan al'amuran Ubangiji, yadda zai gamshe shi.
33 Looli umughosi juno atolile ikuvika mu fiinu fya mu iisi, ndavule lunoghile pikumovosia umunu ghwa mwene,
Amma mai aure yana tunani akan al'amuran duniya, yadda za ya gamshi matarsa,
34 aghaving'ine. Umumama juno natolilue minja vuvule ikuvika nifiinu fya Mutwa, ndavule lunoghile ku lekeng'ana mum'biili na munhumbula. looli umumama juno atolilue ikuvika mu finhu fya mu iisi, ndavule lunoghile pikumovosia umughosi ghwa mwene.
hankalinsa ya rabu. Mace marar aure ko budurwa tana tunanin al'amuran Ubangiji, yadda za ta kebe kanta a jiki da ruhu. Amma mace mai aure tana tunanin al'amuran duniya, yadda za ta gamshi mijinta.
35 Nijova vulevule kuuti luvumbulilo lwinu jumue, nakwekuuti nivateghile ulutegho umue. Nijova vulevule ulwakuuva sa kyang'haani, ulwa kuuti lunoghile pikuvika vavombi kwa Mutwa kisila kikuvasi kyokyoni.
Ina fadar wannan domin amfaninku ne, ba domin in takura ku ba. Na fadi wannan domin abinda ke daidai, yadda zaku bi Ubangiji ba tare da hankalinku ya rabu ba.
36 Nave umuunhu isagha ikunua kukum'bombela nhu vWAoghopua uminja ghwa mwene, vwimila vwa masaghe gha mweene ghaliningufu kyongo, muleke atolanaghe na ghwope ndavule ighanile. Nakwekuuti nyivi.
Amma idan wani yana tunani da cewa baya yin abinda ya dace ga budurwarsa- idan ta wuce shekarun aure, kuma hakan ya zama dole- sai yayi abinda yake so. Ba zunubi yake yi ba. Sai suyi aure.
37 Looli nave mulamuile ulwa kuleka kutola, nakwekuuti ikwumilisivua, nambe nave akagwile pikuvutema uvunoghelua vwa mwene, iva avombile vunofu nambe aleke pikuntola.
Amma idan ya tsaya da karfi a zuciyarsa, idan baya shan wani matsi kuma yana iya kame kansa, har ya kudurta a zuciyarsa yayi haka, wato ya kiyaye budurwarsa da yake tashi, to hakan ya yi daidai.
38 Pa uluo, juno ikuntola uminja ghwa mwene ivomba vunofu, ghweni juno asalwile kuleka kutola iva avombile vunofu.
Don haka, shi wanda ya auri budurwarsa yayi daidai, sannan shi wanda ya zabi yaki yin aure yafi yin daidai.
39 Umumama akungilue numugosi ghwa mwene ye ajighe mwumi. Looli nave umughosi afwile, mwavuke kutolua kwa muunhu ghweni juno amughanile, looli mu mwa Mutwa mwene.
Mace tana a daure ga mijinta a duk tsawon rayuwarsa. Amma idan mijin ya mutu, tana da 'yanci ta auri duk wanda take so ta aura, amma a cikin Ubangiji.
40 Nikyale muvulamusi vwango, iva nulukelo kyongo nave ikale ndavule alivuo. Najune nisagha kuuti nili nu Mhepo ghwa Nguluve.
Amma a ganina, za ta fi farinciki idan za ta zauna yadda take. Kuma ina tunanin ni ma ina da Ruhun Allah.