< Hesekiel 1 >
1 Uti tretionde årena, på femte dagen i fjerde månadenom, då jag var ibland de fångna vid den älfvena Chebar, öppnade sig himmelen, och Gud viste mig syner.
A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
2 Den samme femte dagen var uti femte årena, efter att Jojachin, Juda Konung, var fången bortförd.
A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
3 Då skedde Herrans ord till Hesekiel, Busi son, Prestens, uti de Chaldeers lande, vid den älfvena Chebar; der kom Herrans hand öfver honom.
maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
4 Och jag såg, och si, der kom ett stormväder nordanefter, med en stor molnsky full med eld, så att det glimmade allt omkring; och midt uti eldenom var det ganska klart.
Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
5 Och derinnan uti var lika som fyra djur, och ett af dem var såsom en menniska.
a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
6 Och de hade hvartdera fyra ansigte och fyra vingar.
amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
7 Och deras ben stodo rätt; men deras fötter voro lika som oxafötter, och glimmade såsom glödande koppar;
Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
8 Och hade menniskohänder under deras vingar, på deras fyra sidor; ty de hade alle fyra deras ansigte och deras vingar.
A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
9 Och vingarna voro ju hvar vid annan; och då de gingo, så behöfde de intet vända sig, utan hvart de gingo, gingo de rätt framåt.
kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
10 Deras ansigte på högre sidone af de fyra voro lika som menniskos och lejons; men på venstra sidone af de fyra voro deras ansigte lika som oxars och örns.
Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
11 Och deras ansigte och vingar voro ofvantill uträckte, så att ju två vingar tillsammans slogo, och med två vingar skylde de sina kroppar.
Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
12 Hvart de gingo, då gingo de rätt framåt och de gingo dit som vädret bar, och behöfde intet vända sig, då de gingo.
Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
13 Och djuren voro anseende lika som dödande kol, de der brinna, och lika som bloss emellan djuren; men elden gaf ett glimmande ifrå sig, och utur eldenom gick ett ljungande.
Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
14 Och djuren lupo hit och dit, lika som en ljungeld.
Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
15 Som jag nu så såg dessa djuren, si, då stod der ett hjul på jordene när de fyra djuren, och var anseendes lika som fyra hjul.
Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
16 Och de hjulen voro lika som en turkos, och voro alla fyra, det ena som det andra; och de voro anseende lika som ett hjul vore i de andro.
Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
17 När de skulle gå, så kunde de gå på alla fyra sidor, och behöfde intet vända sig, när de gingo.
Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
18 Deras lötar och höjd voro förskräckelig, och deras lötar voro full med ögon allt omkring på alla fyra hjulen.
Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
19 Och när djuren gingo, så gingo ock hjulen när dem; och då djuren upplyfte sig ifrå jordene, så upplyfte ock hjulen sig.
Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
20 Hvart vädret gick, dit gingo de ock, och hjulen upplyfte sig med dem; ty ett starkt väder var i hjulomen.
Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
21 När de gingo, så gingo desse ock; när de stodo, så stodo desse ock; och när de upplyfte sig ifrå jordene, så upplyfte sig i ock hjulen när dem; ty ett starkt väder var i hjulomen.
Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
22 Men ofvanpå djuren var lika som himmelen, såsom en christall, förskräckelig, rätt öfver dem utsträckt;
A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
23 Så att under himmelen stodo deras vingar, den ene rätt emot den andra; och två vingar öfvertäckte hvarsderas kropp.
A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
24 Och jag hörde vingarna dåna, lika som stor vatten, och lika som en dön dens Allsmägtigas, när de gingo, och lika som en gny af enom här; men när de stilla stodo, så läto de vingarna neder.
Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
25 Och när de stilla stodo, och läto vingarna neder, så dundrade i himmelen öfver dem.
Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
26 Och öfver himmelen, som öfver dem var, var lika som en saphir, såsom en stol, och på dem stolenom satt en, lik ene mennisko.
A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
27 Och jag såg, och det var såsom ett klart ljus; och innantill var det såsom en eld allt omkring; ifrå hans länder upp och neder såg jag såsom en eld blänka allt omkring.
Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
28 Lika som regnbågen synes i molnskynom, när regnat hafver, så blänkte det allt omkring. Detta var Herrans härlighets anseende; och då jag det sett hade, föll jag uppå mitt ansigte, och hörde en tala.
Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.