< Daniel 1 >
1 Uti tredje årena af Jojakims, Juda Konungs, rike kom NebucadNezar, Konungen i Babel, in för Jerusalem, och belade det.
A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
2 Och Herren gaf Jojakim, Juda Konung, honom i händer, och en hop af kärile utu Guds hus; hvilken han lät föra in uti Sinears land, i sins guds hus, och lade de kärilen uti sins guds fatabur.
Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
3 Och Konungen sade till Aspenas, sin öfversta kamererare, att han skulle utsöka honom af Israels barnom, af Konungsliga slägt, och herrabarnom,
Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
4 Några unga drängar, som ingen vank hade; utan dägelige voro, förnuftige, vise, kloke och förståndige; hvilke skickelige voro till att tjena i Konungens gård, och till att lära Chaldeiska skrift och mål.
Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
5 Dessom beställde Konungen, hvad man dem dageliga gifva skulle af hans spis, och af det vin der han sjelf af drack; på det att, då de så i tre år uppfödde voro, skulle de sedan tjena inför Konungenom.
Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
6 Så voro ibland dem Daniel, Hanania, Misael och Asaria, af Juda barnom.
Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
7 Och den öfverste kamereraren gaf dem namn; och nämnde Daniel Beltesazar, och Hanania Sadrach, och Misael Mesach, och Asaria AbedNego.
Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
8 Men Daniel satte sig före i sitt hjerta, att han icke ville orena sig med Konungens spis, och med det vin, som han sjelf drack; och bad öfversta kamereraren, att han icke skulle orena sig.
Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
9 Och Gud gaf Daniel, att öfverste kamereraren vardt honom gunstig och god.
Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
10 Och han sade till honom: Jag fruktar för min Herra Konungen, den eder spis och dryck bestyrt hafver; om han får se, att edor ansigte äro magrare än de andra drängers, som eder jemnåldrige äro, så gören I mig brottsligan till döden inför Konungenom.
amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
11 Då sade Daniel till Melzar, hvilkom öfverste kamereraren Daniel, Hanania, Misael och Asaria, befallt hade:
Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
12 Försök dock der med dina tjenare i tio dagar, och låt gifva oss mos till att äta, och vatten till att dricka;
“Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
13 Och låt alltså komma för dig vår och de andra drängers ansigte, som af Konungens spis äta; och efter som du då ser, derefter gör med dina tjenare.
Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
14 Och han hörde dem derutinnan, och försökte det med dem i tio dagar.
Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
15 Och efter de tio dagar voro de dägeligare och bättre vid hull, än alle de dränger, som spisades af Konungens spis.
A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
16 Så satte Melzar bort deras spis och dryck, den dem tillskickad var, och gaf dem mos.
Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
17 Men dessa fyras Gud gaf dem konst och förstånd uti allahanda skrift och vishet; men Daniel gaf han förstånd i alla syner och drömmar.
Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
18 Då tiden förlupen var, som Konungen förelagt hade, att de skulle hafvas inför honom, hade öfverste kamereraren dem in för NebucadNezar.
A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
19 Och Konungen talade med dem; och vardt ingen ibland dem alla funnen, som Daniels, Hanania, Misaels och Asaria like var; och de vordo Konungens tjenare.
Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
20 Och Konungen fann dem i alla saker, de han dem frågade, tio sinom klokare och förståndigare, än alla stjernokikare och visa i hela sino rike.
A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
21 Och lefde Daniel intill Konung Cores första år.
Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.