< Zaburi 44 >

1 Kwa mwimbishaji. Utenzi wa wana wa Kora. Ee Mungu, tumesikia kwa masikio yetu, baba zetu wametueleza yale uliyotenda katika siku zao, siku za kale.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Kwa mkono wako uliwafukuza mataifa na ukawapanda baba zetu, uliangamiza mataifa na kuwastawisha baba zetu.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Sio kwa upanga wao waliipata nchi, wala si mkono wao uliwapatia ushindi; ilikuwa ni kitanga cha mkono wako wa kuume, na nuru ya uso wako, kwa kuwa uliwapenda.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Wewe ni mfalme wangu na Mungu wangu, unayeamuru ushindi kwa Yakobo.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Kwa uwezo wako tunawasukuma nyuma watesi wetu; kwa jina lako tunawakanyaga adui zetu.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Siutumaini upinde wangu, upanga wangu hauniletei ushindi;
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 bali wewe unatupa ushindi juu ya adui zetu, unawaaibisha watesi wetu.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Katika Mungu wetu tunajivuna mchana kutwa, nasi tutalisifu jina lako milele.
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Lakini sasa umetukataa na kutudhili, wala huendi tena na jeshi letu.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Umetufanya turudi nyuma mbele ya adui, nao watesi wetu wametuteka nyara.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Umetuacha tutafunwe kama kondoo na umetutawanya katika mataifa.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Umewauza watu wako kwa fedha kidogo, wala hukupata faida yoyote kwa mauzo yao.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Umetufanya lawama kwa jirani zetu, dharau na dhihaka kwa wale wanaotuzunguka.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Umetufanya kuwa mithali miongoni mwa mataifa, mataifa hutikisa vichwa vyao.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Fedheha yangu iko mbele yangu mchana kutwa, na uso wangu umejaa aibu tele,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 kwa ajili ya dhihaka ya wale wanaonilaumu na kunitukana, kwa sababu ya adui, ambaye anatamani kulipiza kisasi.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Hayo yote yametutokea, ingawa tulikuwa hatujakusahau wala hatujaenda kinyume na agano lako.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Mioyo yetu ilikuwa haijarudi nyuma; nyayo zetu zilikuwa hazijaiacha njia yako.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Lakini ulituponda na kutufanya makao ya mbweha, na ukatufunika kwa giza nene.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Kama tungalikuwa tumelisahau jina la Mungu wetu au kunyooshea mikono yetu kwa mungu mgeni,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 je, Mungu hangaligundua hili, kwa kuwa anazijua siri za moyo?
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Hata hivyo kwa ajili yako tunauawa mchana kutwa; tumehesabiwa kama kondoo wa kuchinjwa.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Amka, Ee Bwana! Kwa nini unalala? Zinduka! Usitukatae milele.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Kwa nini unauficha uso wako na kusahau taabu na mateso yetu?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Tumeshushwa hadi mavumbini, miili yetu imegandamana na ardhi.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Inuka na utusaidie, utukomboe kwa sababu ya upendo wako usio na mwisho.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Zaburi 44 >