< Isaías 8 >
1 Y el Señor me dijo: Toma una tabla grande, y en él escribe letras comunes, Maher-salal-hasbaz; muy pronto habrá saqueo y destrucción.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 Y tomen verdaderos testigos de lo que está escrito: Urías, sacerdote, y Zacarías, hijo de Jeberquerias.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Me uní con mi mujer, y ella quedó embarazada y dio a luz un hijo. Entonces el Señor me dijo: Dale el nombre Maher-salal-hasbaz,
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 Porque antes de que el niño pueda decir, Padre, o Madre, la riqueza de Damasco y los bienes de Samaria serán quitados por el rey de Asiria.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Y el Señor me dijo de nuevo:
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Porque este pueblo ha aborrecido las aguas que fluyen suavemente de Siloé, temerán a Rezín y al hijo de Remalías;
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 Por esta causa, el Señor les está enviando las aguas del río, profundas y fuertes, hasta el rey de Asiria y toda su gloria: y saldrá por todas sus corrientes, desbordando todos sus bordes.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 Y vendrá a Judá; corriendo y desbordando, hasta que las aguas están hasta el cuello; será como un ave con sus alas extendidas cubrirán la tierra de lado a lado, Emmanuel, porque Dios está con nosotros.
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Ten conocimiento, pueblos, y ten miedo; Escucha, todas las partes lejanas de la tierra: prepárense porque serán destruidos, prepárense porque serán destruidos.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 Tomen consejo, y se convertirán en nada; Da tus órdenes, y no se harán efectivas; porque Dios está con nosotros.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Porque el Señor, me hablo con mano fuerte, me dio órdenes de no ir por el camino de este pueblo, diciendo:
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 No digas: Es conspiración, sobre todo lo que dice este pueblo: Es conspiración; y no tengas miedo de lo que temen ellos.
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 Pero el Señor de los ejércitos sea santo para ti, y teman a él, la reverencia sea para el.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 Y será por lugar santo; pero piedra de tropiezo y una piedra de angustia para las dos casas de Israel y para los hombres de Jerusalén, por lazo y red en la cual puedan ser capturados.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Y muchos de ellos tropezarán allí, caerán y serán quebrantados, y serán enlazados capturados en la red.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Ata el testimonio, sella la ley entre mis discípulos.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 Y esperaré al Señor, cuyo rostro está velado de la casa de Jacob, y lo estaré buscando.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Mira, yo y los hijos que el Señor me ha dado, somos por señales y por maravillas en Israel del Señor de los ejércitos, cuyo lugar de descanso está en el Monte Sión.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 Y cuando te dicen: busca a los que tienen espíritus familiares, y a los adivinos, que susurran y murmuran; ¿No es correcto que un pueblo haga una petición a su dios, Apelará por los vivos a los muertos?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 Entonces diles: Pon tu fe en la enseñanza y en el testimonio. Si no dicen tales palabras. Para él no hay amanecer.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 Y pasará por la tierra con amargas dificultades y en necesidad de alimento; y cuando no pueda comer, se enojará, maldiciendo a su rey y a su Dios, y sus ojos se volverán al cielo en lo alto;
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 Y él estará mirando hacia abajo en la tierra, y habrá problemas y serán lanzados a nubes oscuras, noche negra donde no hay visión.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.