< Isaías 7 >

1 Aconteció en los días de Acaz, hijo de Jotam, hijo de Uzías, rey de Judá, que llegaron Rezín, rey de Aram, y Peka, hijo de Remalías, rey de Israel. Hasta Jerusalén para hacer la guerra contra ella, pero no pudieron vencerla.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 Y llegó a la familia de David la noticia de que Aram había levantado sus tiendas en Efraín. Y el corazón del rey y los corazones de su pueblo se conmovieron, como los árboles del bosque temblando en el viento.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Entonces el Señor le dijo a Isaías: Sal ahora, tú y Sear-jasub, tu hijo, y te encontrarás con Acaz al final de la corriente que fluye desde el estanque más alto, en la carretera del campo del lavandero;
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 Y dile: Cuídate y ten calma; no temas, y no dejes que tu corazón se debilite, debido a estos dos carbones humeantes, debido a la amarga ira de Rezín y Aram, y del hijo de Remalías.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Porque Aram ha tramado mal contra ti, diciendo:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 Subamos contra Judá a invadir y aterroricemosla, y pongamos en ella un rey, el hijo de Tabeel.
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Esta es la palabra del Señor Dios: Esto jamas se realizará.
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 Porque la cabeza de Aram es Damasco, y la cabeza de Damasco es Rezín y dentro de sesenta y cinco años desde ahora, Efraín será quebrantado, y ya no será un pueblo:
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Y la cabeza de Efraín es Samaria, y la cabeza de Samaria es el hijo de Remalías. Si no lo creen, tu reino no permanecerá.
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 Entonces Isaías volvió a decir a Acaz:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 Pide al Señor tu Dios una señal, una señal en los lugares profundos del inframundo o en los cielos altos. (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 Pero Acaz dijo: No pondré a prueba al Señor haciendo tal petición.
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Y él dijo: Escucha ahora, oh familia de David: ¿no es suficiente que estés llevando a los hombres al disgusto? ¿Harás lo mismo con mi Dios?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 Por esta causa, el mismo Señor te dará una señal; una joven ahora está embarazada, y ella dará a luz un hijo, y ella le dará el nombre de Emanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 La cuajada y la miel serán su alimento, cuando tenga la edad suficiente para tomar una decisión entre el mal y el bien.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 Porque antes de que el niño tenga la edad suficiente para tomar una decisión entre el mal y el bien, la tierra cuyos dos reyes que ahora temen se habrá convertido en un desperdicio.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 El Señor está a punto de enviarte a ti, a tu pueblo y a la casa de tu padre, un tiempo de angustia que no ha habido desde los días de la separación de Efraín de Judá; Incluso la venida del rey de Asiria.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 Y será en ese día que el Señor hará un sonido para la mosca que está al final de los ríos de Egipto, y para la abeja que está en la tierra de Asiria.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 Y vendrán, cubriendo todos los valles desolados, y los agujeros de las rocas, y las espinas, y todos los lugares de riego.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 En ese día, el Señor rasurara el pelo de la cabeza y de los pies, así como el pelo de la cara, con una cuchilla alquilada del otro lado del río; con el rey de Asiria.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 Y será en ese día que un hombre dará comida a una vaca joven y dos ovejas;
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 Y darán tanta leche que él podrá tener cuajada para su comida; porque la cuajada y la miel serán la comida de todos los que aún viven en la tierra.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 Y será en ese día que en todos los lugares donde antes había mil vides valoradas en mil siclos de plata, no habrá más que maleza y espinas.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 Los hombres vendrán allí con arcos y flechas, porque toda la tierra estará llena de maleza y espinos.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 Y enviarán los bueyes y las ovejas a todas las colinas que antes se trabajaban con azadón, porque solo es espinos y maleza y servirán solo para pastizales.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaías 7 >