< Nehemías 11 >

1 Los príncipes del pueblo vivían en Jerusalén. El resto del pueblo también echó suertes para que uno de los diez habitara en Jerusalén, la ciudad santa, y nueve partes en las demás ciudades.
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
2 El pueblo bendijo a todos los hombres que se ofrecieron voluntariamente para habitar en Jerusalén.
Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
3 Estos son los jefes de la provincia que vivían en Jerusalén; pero en las ciudades de Judá, cada uno vivía en su posesión en sus ciudades: los sacerdotes, los levitas, los servidores del templo y los hijos de los servidores de Salomón.
Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
4 Algunos de los hijos de Judá y de los hijos de Benjamín vivían en Jerusalén. De los hijos de Judá Ataías hijo de Uzías, hijo de Zacarías, hijo de Amarías, hijo de Sefatías, hijo de Mahalalel, de los hijos de Fares;
yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
5 y Maasías hijo de Baruc, hijo de Colhoze, hijo de Hazaías, hijo de Adaías, hijo de Joiarib, hijo de Zacarías, hijo del silonita.
da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
6 Todos los hijos de Fares que vivían en Jerusalén eran cuatrocientos sesenta y ocho hombres valientes.
Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
7 Estos son los hijos de Benjamín: Salú, hijo de Mesulam, hijo de Joed, hijo de Pedaías, hijo de Colaías, hijo de Maasías, hijo de Itiel, hijo de Jesaías.
Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
8 Después de él, Gabbai y Sallai, novecientos veintiocho.
da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
9 Joel hijo de Zicri era su supervisor; y Judá hijo de Hasenúa era el segundo sobre la ciudad.
Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
10 De los sacerdotes: Jedaías hijo de Joiarib, Jacín,
Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
11 Seraías hijo de Hilcías, hijo de Mesulam, hijo de Sadoc, hijo de Meraiot, hijo de Ahitub, jefe de la casa de Dios,
da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
12 y sus hermanos que hacían la obra de la casa, ochocientos veintidós; y Adaías hijo de Jeroham, hijo de Pelalías, hijo de Amzi, hijo de Zacarías, hijo de Pashur, hijo de Malquías,
tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
13 y sus hermanos, jefes de las casas paternas, doscientos cuarenta y dos y Amashsai hijo de Azarel, hijo de Ahzai, hijo de Meshillemoth, hijo de Immer,
da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
14 y sus hermanos, hombres valientes, ciento veintiocho; y su jefe era Zabdiel, hijo de Haggedolim.
da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
15 De los levitas Semaías hijo de Hasub, hijo de Azricam, hijo de Hasabías, hijo de Bunni;
Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
16 y Sabetai y Jozabad, de los jefes de los levitas, que tenían a su cargo los asuntos externos de la casa de Dios;
da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
17 y Matanías hijo de Mica, hijo de Zabdi, hijo de Asaf, que era el jefe que iniciaba la acción de gracias en la oración, y Bacbuquías, el segundo entre sus hermanos; y Abda hijo de Sammúa, hijo de Galal, hijo de Jedutún.
Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
18 Todos los levitas de la ciudad santa eran doscientos ochenta y cuatro.
Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
19 Además, los guardianes de las puertas, Acub, Talmón y sus hermanos, que vigilaban las puertas, eran ciento setenta y dos.
Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
20 El resto de Israel, de los sacerdotes y de los levitas, estaban en todas las ciudades de Judá, cada uno en su heredad.
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21 Pero los servidores del templo vivían en Ofel, y Ziha y Gishpa estaban al frente de los servidores del templo.
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22 El supervisor de los levitas en Jerusalén era Uzi hijo de Bani, hijo de Hasabías, hijo de Matanías, hijo de Mica, de los hijos de Asaf, los cantores, estaba a cargo de los asuntos de la casa de Dios.
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23 Porque había un mandamiento del rey acerca de ellos, y una provisión establecida para los cantores, como cada día lo requería.
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24 Petaías, hijo de Meshezabel, de los hijos de Zera, hijo de Judá, estaba al lado del rey en todos los asuntos del pueblo.
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
25 En cuanto a las aldeas con sus campos, algunos de los hijos de Judá vivían en Quiriat Arba y sus pueblos, en Dibón y sus pueblos, en Jekabzeel y sus aldeas,
Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
26 en Jesúa, en Moladah, Bet Pelet,
Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
27 en Hazar Shual en Beersheba y sus aldeas,
da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
28 en Ziklag, en Meconah y sus aldeas,
Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
29 en En Rimmon, en Zorah, en Jarmuth,
Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
30 Zanoah, Adullam y sus aldeas, Lachish y sus campos, y Azekah y sus aldeas. Y acamparon desde Beerseba hasta el valle de Hinom.
da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
31 Los hijos de Benjamín también vivían desde Geba, en Micmas y Aija, y en Betel y sus pueblos,
Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
32 en Anatot, Nob, Ananías,
da Anatot, da Nob, da Ananiya,
33 Hazor, Ramá, Gittaim,
da Hazor, da Rama, da Gittayim,
34 Hadid, Zeboim, Neballat,
da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
35 Lod y Ono, el valle de los artesanos.
da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
36 De los levitas, ciertas divisiones de Judá se establecieron en el territorio de Benjamín.
Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.

< Nehemías 11 >