< 1 Samuel 12 >

1 Samuel je rekel vsemu Izraelu: »Glejte, prisluhnil sem vašemu glasu v vsem, kar ste mi rekli in postavil sem kralja nad vami.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 In sedaj glejte, kralj hodi pred vami. Jaz pa sem starec in sivolas in glejte, moja sinova sta z vami. Hodil sem pred vami od svojega otroštva, do tega dne.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Glejte, tukaj sem. Pričujte zoper mene pred Gospodom in pred njegovim maziljencem. Čigavega vola sem vzel? Ali čigavega osla sem vzel? Ali sem koga ogoljufal? Koga sem zatiral? Ali iz čigave roke sem sprejel kakršnokoli podkupnino, da bi mi s tem zaslepil oči? In povrnil vam bom.«
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Rekli so: »Nisi nas ogoljufal niti nas nisi zatiral niti nisi vzel karkoli iz roke kateregakoli moža.«
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Rekel jim je: » Gospod je priča zoper vas in njegov maziljenec je priča ta dan, da v moji roki niste našli ničesar.« Odgovorili so: » On je priča.«
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Samuel je ljudstvu rekel: » Gospod je ta, ki je določil Mojzesa in Arona in ki je vaše očete privedel gor iz egiptovske dežele.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Zdaj torej mirno stojte, da se bom lahko pravdal z vami pred Gospodom o vseh pravičnih dejanjih Gospoda, ki jih je storil vam in vašim očetom.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 Ko je Jakob prišel v Egipt in so vaši očetje klicali h Gospodu, potem jim je Gospod poslal Mojzesa in Arona, ki sta vaše očete privedla ven iz Egipta in jim dala prebivati na tem kraju.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 Ko pa so pozabili Gospoda, svojega Boga, jih je prodal v roko Siserája, poveljnika Hacórjeve vojske in v roko Filistejcev in v roko moábskega kralja in so se borili zoper njih.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Klicali so h Gospodu in rekli: ›Grešili smo, ker smo zapustili Gospoda in smo služili Báalom in Astarti. Toda sedaj nas osvobodi iz roke naših sovražnikov in mi ti bomo služili.‹
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 Gospod je poslal Jerubáala, Bedána, Jefteja in Samuela in vas osvobodil iz roke vaših sovražnikov na vsaki strani in vi ste varno prebivali.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 Ko pa ste videli, da je proti vam prišel Naháš, kralj Amónovih otrok, ste mi rekli: ›Ne, temveč bo kralj kraljeval nad nami.‹ Ko je bil Gospod, vaš Bog, vaš kralj.
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 Zdaj torej glejte kralja, ki ste ga izbrali in ki ste si ga želeli! In glejte, Gospod je postavil kralja nad vami.
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 Če se boste bali Gospoda in mu služili in ubogali njegov glas in se ne boste uprli zoper Gospodovo zapoved, potem boste tako vi kot vaš kralj, ki kraljuje nad vami, še naprej sledili Gospodu, svojemu Bogu.
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 Toda če ne boste ubogali glasu Gospoda, temveč se boste uprli zoper Gospodovo zapoved, potem bo Gospodova roka zoper vas, kakor je bila zoper vaše očete.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 Zdaj torej stojte in vidite to veliko stvar, ki jo bo Gospod storil pred vašimi očmi.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 Mar ni danes pšenična žetev? Klical bom h Gospodu in poslal bo grmenje in dež, da boste lahko zaznali in videli, da je vaša zlobnost velika, ki ste jo storili v Gospodovih očeh, v tem, da ste si zahtevali kralja.«
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Tako je Samuel zaklical h Gospodu in Gospod je ta dan poslal grmenje in dež, in vse ljudstvo se je silno balo Gospoda in Samuela.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 Vse ljudstvo je reklo Samuelu: »Moli za svoje služabnike h Gospodu, svojemu Bogu, da ne umremo, kajti vsem svojim grehom smo dodali to zlo, da smo si zahtevali kralja.«
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Samuel je ljudstvu rekel: »Ne bojte se. Storili ste vso to zlobnost, vendar se ne obrnite stran od sledenja Gospodu, temveč z vsem svojim srcem služite Gospodu
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 in ne obrnite se stran, kajti potem bi šli za praznimi stvarmi, ki ne morejo koristiti niti osvoboditi, kajti prazne so.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 Kajti Gospod ne bo zapustil svojega ljudstva zaradi svojega veličastnega imena, ker je Gospodu ugajalo, da vas naredi za svoje ljudstvo.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Poleg tega, kar se mene tiče, Bog ne daj, da bi grešil zoper Gospoda v [tem], da bi prenehal moliti za vas, temveč vas bom učil dobro in pravilno pot.
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 Samo bojte se Gospoda in mu služite v resnici, z vsem svojim srcem, kajti preudarite kako velike stvari je storil za vas.
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 Toda če boste še vedno počeli zlobno, boste použiti, tako vi kakor vaš kralj.«
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.

< 1 Samuel 12 >