< 1 Samuel 11 >
1 Potem je prišel gor Amónec Naháš in se utaboril zoper Jabéš Gileád. Vsi možje Jabéša so rekli Nahášu: »Skleni zavezo z nami in mi ti bomo služili.«
Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
2 Amónec Naháš jim je odgovoril: »Pod tem pogojem bom sklenil zavezo z vami, da vam lahko iztaknem vsa vaša desna očesa in to položim za grajo nad ves Izrael.«
Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
3 Starešine iz Jabéša so mu rekli: »Daj nam sedem dni predaha, da lahko odpošljemo poslance v vse Izraelove pokrajine, in potem, če ne bo nobenega človeka, da nas reši, bomo prišli ven k tebi.«
Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
4 Potem sta poslanca prišla v Savlovo Gíbeo in v ušesa ljudstva povedala novice in vse ljudstvo je povzdignilo svoje glasove ter zajokalo.
Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
5 Glej, Savel je prišel za čredo iz polja in Savel je rekel: »Kaj pesti ljudstvo, da jokajo?« Povedali so mu novice od ljudi iz Jabéša.
A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
6 Božji Duh je prišel nad Savla, ko je slišal tiste novice in njegova jeza je bila silno vneta.
Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
7 Snel je jarem iz volov in ju razsekal na koščke in le-te poslal po vseh Izraelovih pokrajinah, po rokah poslancev, rekoč: »Kdorkoli ne pride naprej za Savlom in Samuelom, bo tako storjeno njegovim volom.« Gospodov strah je padel na ljudstvo in prišli so ven soglasno.
Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
8 Ko jih je preštel v Bezeku, je bilo Izraelovih otrok tristo tisoč in Judovih mož trideset tisoč.
Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
9 Poslancem, ki so prišli, so povedali: »Tako boste rekli možem iz Jabéš Gileáda: ›Jutri, ob času, ko sonce postane vroče, boste imeli pomoč.‹« Poslanci so prišli in to pokazali možem iz Jabéša in bili so veseli.
Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
10 Zato so možje iz Jabéša rekli: »Jutri bomo prišli ven k vam in z nami boste lahko storili vse, kar se vam zdi dobro.«
Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
11 Naslednjega dne je bilo to tako, da je Savel ljudstvo razvrstil v tri skupine in prišli so v sredo vojske ob jutranji straži in usmrtili Amónce do dnevne vročine. Pripetilo se je, da so bili tisti, ki so preostali, razkropljeni, tako da niti dva izmed njih nista ostala skupaj.
Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
12 Ljudstvo je reklo Samuelu: »Kdo je tisti, ki je rekel: ›Ali bo Savel kraljeval nad nami?‹ Privedite može, da jih lahko usmrtimo.«
Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
13 Savel je rekel: »Danes ne bo usmrčen noben mož, kajti danes je Gospod izvêdel rešitev duš v Izraelu.«
Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
14 Potem je Samuel rekel ljudstvu: »Pridite in pojdimo v Gilgál in tam obnovimo kraljestvo.«
Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
15 Vse ljudstvo je odšlo v Gilgál in tam, v Gilgálu, so postavili Savla za kralja pred Gospodom in tam so žrtvovali žrtvovanje mirovnih daritev pred Gospodom in tam so se Savel in vsi Izraelovi možje silno veselili.
Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.