< 1 Kralji 12 >

1 Rehabám je odšel v Sihem, kajti ves Izrael je prišel v Sihem, da ga postavijo za kralja.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 Pripetilo se je, ko je Nebátov sin Jerobeám, ki je bil še v Egiptu, slišal o tem (kajti pobegnil je izpred prisotnosti kralja Salomona in je Jerobeám prebival v Egiptu),
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 da so poslali in ga poklicali. Jerobeám in vsa Izraelova skupnost pa je prišla in spregovorila Rehabámu, rekoč:
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 »Tvoj oče je naš jarem naredil boleč. Sedaj torej olajšaj bolečo službo svojega očeta in njegov težek jarem, ki ga je položil na nas in mi ti bomo služili.«
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 Rekel jim je: »Odidite še za tri dni, potem ponovno pridite k meni.« In ljudstvo je odšlo.
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 Kralj Rehabám se je posvetoval s starci, ki so stali pred njegovim očetom Salomonom, medtem ko je še živel in rekel: »Kako svetujete, da lahko odgovorim temu ljudstvu?«
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 Odgovorili so mu, rekoč: »Če hočeš biti ta dan služabnik temu ljudstvu in jim hočeš služiti in jim odgovoriti in jim govoriti dobre besede, potem bodo tvoji služabniki na veke.«
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 Toda zapustil je nasvet starcev, ki so mu ga dali in se posvetoval z mladeniči, ki so odrasli z njim in ki so stali pred njim
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 in jim rekel: »Kakšen nasvet dajete vi, da lahko odgovorimo temu ljudstvu, ki mi je govorilo, rekoč: ›Naredi jarem, ki ga je tvoj oče položil nad nas, lažji?‹«
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 Mladeniči, ki so zrasli z njim, so mu govorili, rekoč: »Tako boš govoril temu ljudstvu, ki ti je govorilo, rekoč: ›Tvoj oče je naš jarem naredil težek, toda ti nam ga olajšaj; ‹ tako jim boš rekel: ›Moj mali prst bo debelejši kakor očetova ledja.
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 Kakor vam je moj oče naložil težek jarem, bom sedaj dodal vašemu jarmu. Moj oče vas je kaznoval z biči, toda jaz vas bom kaznoval s škorpijoni.‹«
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 Tako je Jerobeám in vse ljudstvo tretji dan prišlo k Rehabámu, kakor je kralj določil, rekoč: »Ponovno pridite k meni tretji dan.«
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 Kralj je ljudstvu surovo odgovoril in zapustil nasvet starcev, ki so mu ga dali.
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 Spregovoril jim je glede na nasvet mladeničev, rekoč: »Moj oče je vaš jarem naredil težek, jaz pa bom vašemu jarmu dodal. Moj oče vas je kaznoval tudi z biči, toda jaz vas bom kaznoval s škorpijoni.«
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 Zatorej kralj ni prisluhnil ljudstvu, kajti stvar je bila od Gospoda, da je lahko izpolnil svojo besedo, ki jo je Gospod po Šilčanu Ahíju govoril Nebátovemu sinu Jerobeámu.
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 Torej ko je ves Izrael videl, da jim kralj ni prisluhnil, je ljudstvo odgovorilo kralju, rekoč: »Kakšen delež imamo v Davidu? Niti nimamo dediščine v Jesejevem sinu. K svojim šotorom, oh Izrael. Sedaj poglej k svoji lastni hiši, David.« Tako je Izrael odšel v svoje šotore.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 Toda kar se tiče Izraelovih otrok, ki so prebivali v Judovih mestih, je nad njimi kraljeval Rehabám.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Potem je kralj Rehabám poslal Adoráma, ki je bil nad davkom in ves Izrael ga je kamnal s kamni, da je umrl. Zato je kralj Rehabám pohitel, da se spravi k svojemu bojnemu vozu, da pobegne v Jeruzalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 Tako se je Izrael uprl zoper Davidovo hišo do današnjega dne.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 Pripetilo se je, ko je ves Izrael slišal, da je Jerobeám ponovno prišel, da so poslali in ga poklicali k skupnosti in ga postavili za kralja nad vsem Izraelom. Tam ni bilo nikogar, ki je sledil Davidovi hiši, razen samo Judovega rodu.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 Ko je Rehabám prišel v Jeruzalem, je zbral vso Judovo hišo, z Benjaminovim rodom, sto osemdeset tisoč izbranih mož, ki so bili bojevniki, da se bojujejo zoper Izraelovo hišo, da kraljestvo ponovno privedejo k Salomonovemu sinu Rehabámu.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 Toda beseda od Boga je prišla k Šemajáju, Božjemu možu, rekoč:
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 »Govori Salomonovemu sinu Rehabámu, Judovemu kralju in vsej Judovi in Benjaminovi hiši in preostanku ljudstva, rekoč:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 ›Tako govori Gospod: ›Ne boste šli gor niti se ne boste borili zoper vaše brate, Izraelove otroke. Vsak mož naj se vrne k svoji hiši, kajti ta stvar je od mene.‹« Prisluhnili so torej Gospodovi besedi in se vrnili, da odidejo, glede na Gospodovo besedo.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 Potem je Jerobeám na gori Efrájim zgradil Sihem in tam prebival in odšel od tam ter zgradil Penuél.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 Jerobeám je v svojem srcu rekel: »Sedaj se bo kraljestvo vrnilo k Davidovi hiši.
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
27 Če gre to ljudstvo gor, da opravi klavno daritev v Gospodovi hiši, v Jeruzalemu, potem se bo srce tega ljudstva ponovno obrnilo k njihovemu gospodu, k Judovemu kralju Rehabámu, mene pa bodo ubili in ponovno odšli k Judovemu kralju Rehabámu.«
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 Nakar se je kralj posvetoval in naredil dve teleti iz zlata ter jim rekel: »To je za vas preveč, da greste gor v Jeruzalem. Poglejte svoje bogove, oh Izrael, ki so te privedli gor iz egiptovske dežele.«
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 Eno je postavil v Betelu, drugo pa v Danu.
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 Ta stvar je postala greh, kajti ljudstvo je odšlo, da bi oboževalo pred enim, celó k Danu.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 Naredil je hišo visokih krajev in iz najnižjih izmed ljudstva naredil duhovnike, ki niso bili izmed Lévijevih sinov.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 Jerobeám je odredil praznovanje v osmem mesecu, na petnajsti dan meseca, podobno prazniku, ki je v Judu in daroval na oltarju. Tako je storil v Betelu, žrtvoval je teletoma, ki ju je naredil in v Betelu je postavil duhovnike visokih krajev, ki jih je naredil.
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 Tako je daroval na oltarju, ki ga je naredil v Betelu, na petnajsti dan osmega meseca, celó v mesecu, ki ga je zasnoval iz svojega lastnega srca in odredil praznovanje Izraelovim otrokom in daroval na oltarju in zažgal kadilo.
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Kralji 12 >