< 1 Kralji 11 >
1 Toda kralj Salomon je ljubil mnoge tuje žene, skupaj s faraonovo hčerjo, ženske iz Moába, Amónke, Edómke, Sidónke in Hetejke,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 od narodov glede katerih je Gospod Izraelovim otrokom rekel: »Ne boste vstopili k njim niti oni ne smejo vstopiti k vam, kajti zagotovo bodo vaše srce odvrnili za svojimi bogovi.« Salomon se je v ljubezni trdno pridružil k njim.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Imel je sedemsto žená, princese in tristo priležnic in njegove žene so odvrnile njegovo srce.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Kajti zgodilo se je, ko je bil Salomon star, da so njegove žene njegovo srce odvrnile za drugimi bogovi in njegovo srce ni bilo popolno z Gospodom, njegovim Bogom, kot je bilo srce njegovega očeta Davida.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Kajti Salomon je šel za Astarto, boginjo Sidóncev in za Milkómom, gnusobo Amóncev.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 Salomon je počel zlo v Gospodovih očeh in ni popolnoma šel za Gospodom, kakor je delal njegov oče David.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Potem je Salomon zgradil visok kraj za Kemoša, gnusobo Moábcev, na hribu, ki je pred Jeruzalemom in za Moloha, ogabnost Amónovih otrok.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Podobno je storil za vse svoje tuje žene, ki so zažigale kadilo in žrtvovale svojim bogovom.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 Gospod pa je bil jezen nad Salomonom, ker je bilo njegovo srce odvrnjeno od Gospoda, Izraelovega Boga, ki se mu je dvakrat prikazal
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 in mu je glede te stvari zapovedal, da naj ne gre za drugimi bogovi. Toda tega, kar mu je Gospod zapovedal, ni ohranil.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Zato je Gospod Salomonu rekel: »Ker si to storil in nisi obvaroval moje zaveze in mojih zakonov, ki sem ti jih zapovedal, ti bom zagotovo iztrgal kraljestvo in ga dal tvojemu služabniku.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Vendar zaradi tvojega očeta Davida tega ne bom storil v tvojih dneh, temveč ga bom iztrgal iz roke tvojega sina.
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Toda ne bom odtrgal vsega kraljestva, temveč bom en rod dal tvojemu sinu zaradi Davida, svojega služabnika in zaradi Jeruzalema, ki sem ga izbral.«
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 Gospod je Salomonu razvnel nasprotnika, Edómca Hadáda. Ta je bil iz kraljevega semena v Edómu.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Kajti pripetilo se je, ko je bil David v Edómu in je Joáb, poveljnik vojske, odšel gor, da pokoplje umorjene, potem ko je udaril vsakega moškega v Edómu
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (kajti šest mesecev je Joáb ostal tam z vsem Izraelom, dokler ni iztrebil vsakega moškega v Edómu),
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 da je Hadád pobegnil, on in z njim nekateri Edómci, služabniki njegovega očeta, da gredo v Egipt; Hadád je bil še majhen otrok.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Vstali so iz Midjána in prišli v Parán in s seboj so vzeli može iz Parána ter prišli v Egipt, k faraonu, egiptovskemu kralju, ki mu je dal hišo, mu določil živež in mu dal deželo.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 Hadád je našel veliko naklonjenost v faraonovih očeh, tako da mu je dal za ženo sestro svoje lastne žene, sestro kraljice Tahpenése.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Tahpenésina sestra mu je rodila Genubáta, njegovega sina, ki ga je Tahpenésa vzgajala v faraonovi hiši in Genubát je bil v faraonovi hiši med faraonovimi sinovi.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Ko je Hadád v Egiptu slišal, da je David zaspal s svojimi očeti in da je bil Joáb, poveljnik vojske, mrtev, je Hadád rekel faraonu: »Pusti me oditi, da lahko grem k svoji lastni deželi.«
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 Potem mu je faraon rekel: »Toda kaj ti je manjkalo z menoj, glej, da si prizadevaš, da greš v svojo lastno deželo?« Odgovoril je: »Nič, vendar me vseeno pusti oditi.«
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 Bog pa mu je razvnel drugega nasprotnika, Eljadájevega sina Rezóna, ki je pobegnil pred svojim gospodom Hadadézerjem, kraljem iz Cobe.
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 K sebi je zbral može in postal poveljnik nad četo, ko je David usmrtil tiste iz Cobe in odšli so v Damask, tam prebivali in kraljevali v Damasku.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Vse Salomonove dni je bil nasprotnik Izraelu, poleg vragolije, ki jo je storil Hadád. Preziral je Izrael in kraljeval nad Sirijo.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Jerobeám, Nebátov sin, Efratejec iz Ceréde, Salomonov služabnik (katerega materino ime je bilo Cerúja, vdova), celo on je dvignil svojo roko zoper kralja.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 To je bil razlog, da je svojo roko dvignil zoper kralja. Salomon je zgradil Miló in popravil vrzeli mesta svojega očeta Davida.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 Mož Jerobeám je bil mogočen, hraber človek in Salomon, ko je videl, da je bil mladenič podjeten, ga je postavil za vladarja nad vso zadolžitvijo Jožefove hiše.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 Pripetilo se je ob tistem času, ko je Jerobeám odšel iz Jeruzalema, da ga je na poti našel prerok Šilčan Ahíja, in ta se je odel z novo obleko in onadva sta bila sama na polju.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Ahíja je zgrabil novo obleko, ki je bila na njem in jo raztrgal na dvanajst kosov
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 in rekel Jerobeámu: »Vzemi si deset kosov, kajti tako govori Gospod, Izraelov Bog: ›Glej, iztrgal bom kraljestvo iz Salomonove roke in tebi bom dal deset rodov
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 (toda on bo imel en rod zaradi mojega služabnika Davida in zaradi Jeruzalema, mesta, ki sem ga izbral izmed vseh Izraelovih rodov),
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 zato ker so me zapustili in oboževali Astarto, boginjo Sidóncev, Kemoša, boga Moábcev in Milkóma, boga Amónovih otrok in niso hodili po mojih poteh, da delajo to, kar je pravilno v mojih očeh in da ohranjajo moje zakone in moje sodbe, kakor je počel njegov oče David.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Vendar iz njegove roke ne bom vzel celotnega kraljestva, temveč ga bom zaradi Davida, svojega služabnika, ki sem ga izbral, naredil za princa vse dni njegovega življenja, ker je ohranjal moje zapovedi in moje zakone,
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 toda kraljestvo bom vzel iz roke njegovega sina in ga dal tebi, celó deset rodov.
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 Njegovemu sinu pa bom dal en rod, da bo David, moj služabnik, lahko vedno imel luč pred menoj v Jeruzalemu, mestu, ki sem ga izbral, da tam postavim svoje ime.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Vzel te bom in kraljeval boš glede na vse, kar želi tvoja duša in boš kralj nad Izraelom.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Zgodilo se bo, če boš prisluhnil vsemu, kar ti zapovem in boš hodil po mojih poteh in delal to, kar je pravilno v mojih očeh, da se držiš mojih zakonov in mojih zapovedi, kakor se je moj služabnik David, da bom jaz s teboj in ti bom zgradil zanesljivo hišo, kakor sem jo zgradil za Davida, Izraela pa bom izročil tebi.
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 Zaradi tega bom prizadel Davidovo seme, toda ne na veke.‹«
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Salomon je torej iskal, da ubije Jerobeáma. Jerobeám pa je vstal in pobegnil v Egipt, k egiptovskemu kralju Šišáku in v Egiptu je bil do Salomonove smrti.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Ostala Salomonova dela in vse, kar je storil in njegova modrost, mar niso zapisana v knjigi Salomonovih del.
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Časa, ko je Salomon v Jeruzalemu kraljeval nad vsem Izraelom, je bilo štirideset let.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 Salomon je zaspal s svojimi očeti in bil pokopan v mestu svojega očeta Davida. Namesto njega je zakraljeval njegov sin Rehabám.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.