< Книга пророка Исаии 63 >
1 Кто Сей пришедый от Едома, червлены ризы Его от Восора, Сей красен во утвари, зело с крепостию? Аз глаголю правду и суд спасения.
Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
2 Почто червлены ризы Твоя и одежды Твоя яко от истоптания точила?
Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
3 Исполнен истоптания, и от язык несть мужа со Мною: и попрах я яростию Моею, и сотрох я яко персть, и сведох кровь их в землю и вся ризы Моя омочих:
“Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
4 день бо воздаяния прииде на них, и лето избавления приспе:
Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
5 и воззрех, и не бе помощника: и помыслих, и никтоже заступи: и избави я мышца Моя, и ярость Моя наста:
Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
6 и попрах я гневом Моим и сведох кровь их в землю.
Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
7 Милость Господню помянух, добродетели Господни во всех, имиже нам воздает: Господь, судия благ дому Израилеву, наводит нам по милости Своей и по множеству правды Своея.
Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
8 И рече: не людие ли Мои? Чада, и не отвергнутся. И бысть им во спасение и всякия скорби их.
Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
9 Не ходатай, ниже Ангел, но Сам Господь спасе их, зане любит их и щадит их: Сам избави их и восприят их и вознесе их во вся дни века.
Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
10 Тии же не покоришася и разгневаша Духа Святаго Его, и обратися им на вражду, и Той воева на ня.
Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
11 И помяну дни вечныя: где возведый от земли пастыря овец Своих? Где есть вложивый в них Духа Святаго?
Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
12 Возведшая десницею Моисеа, мышца славы Его раздели воду пред лицем его сотворити Ему имя вечно,
wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
13 проведе их сквозе бездну, якоже коня сквозе пустыню, и не утрудишася,
wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
14 и яко скоты по полю, и сниде Дух от Господа и настави их: тако провел еси люди Твоя сотворити Тебе Самому имя славно.
kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
15 Обратися, Господи, от небесе и виждь от дому святаго Твоего и славы Твоея: где есть ревность Твоя и крепость Твоя? Где есть множество милости Твоея и щедрот Твоих, яко терпел еси нам?
Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
16 Ты бо еси Отец наш, понеже Авраам не уведе нас, и Израиль не позна нас, но Ты, Господи, Отец наш, избави ны, исперва имя Твое на нас есть.
Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
17 Что уклонил еси нас, Господи, от пути Твоего? И ожесточил еси сердца наша, еже не боятися Тебе? Обратися ради раб Твоих, ради племен достояния Твоего,
Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
18 да (поне) мало наследим горы святыя Твоея. Противницы наши попраша святыню Твою:
Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
19 быхом яко исперва, егда не владел еси нами, ниже бе наречено имя Твое на нас.
Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.