< Откривење 12 >

1 И знак велики показа се на небу: жена обучена у сунце, и месец под ногама њеним, и на глави њеној венац од дванаест звезда.
Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta.
2 И беше трудна, и викаше од муке, и мучаше се да роди.
Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa.
3 И показа се други знак на небу, и гле, велика црвена аждаха, која имаше седам глава, и десет рогова; и на главама њеним седам круна;
Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa.
4 И реп њен одвуче трећину звезда небеских, и баци их на земљу. И аждаха стајаше пред женом која хтеде да се породи, да јој прождере дете кад роди.
Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi.
5 И роди мушко, сина, који ће пасти све народе с палицом гвозденом; и дете њено би узето к Богу и престолу његовом.
Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa.
6 А жена побеже у пустињу где имаше место приправљено од Бога, да се онамо храни хиљаду и двеста и шездесет дана.
Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.
7 И поста рат на небу. Михаило и анђели Његови ударише на аждаху, и би се аждаха и анђели њени.
Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani.
8 И не надвладаше, и више им се не нађе места на небу.
Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama.
9 И збачена би аждаха велика, стара змија, која се зове ђаво и сотона, која вара сав васиони свет, и збачена би на земљу, и анђели њени збачени бише с њом.
Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.
10 И чух глас велики на небу који говори: Сад поста спасење и сила и царство Бога нашег, и област Христа Његовог; јер се збаци опадач браће наше, који их опадаше пред Богом нашим дан и ноћ.
Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
11 И они га победише крвљу Јагњетовом и речју сведочанства свог, и не марише за живот свој до саме смрти.
Sun ci nasara a kansa ta wurin jinin Ɗan Ragon da ta wurin kalmar shaidarsu; ba su ƙaunaci rayukansu sosai har da za su ja da baya daga mutuwa.
12 Зато веселите се небеса и ви који живите на њима. Тешко вама који живите на земљи и мору, јер ђаво сиђе к вама, и врло се расрдио, знајући да времена мало има.
Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai, da ku da kuke zaune a cikinsu! Amma kaiton duniya da kuma teku, gama Iblis ya sauko gare ku! Ya cika da fushi, domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”
13 И кад виде аждаха да збачена би на земљу, гоњаше жену која роди мушко.
Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji.
14 И жени дана бише два крила орла великог да лети у пустињу на своје место, где ће се хранити време и времена и по времена, сакривена од лица змијиног.
Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba.
15 И испусти змија за женом из уста својих воду као реку, да је утопи у реци.
Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya.
16 И поможе земља жени, и отвори земља уста своја, и прождре реку коју испусти змија из уста својих.
Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa.
17 И разгневи се змија на жену, и отиде да се побије са осталим семеном њеним, које држи заповести Божије и има сведочанство Исуса Христа.
Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.

< Откривење 12 >