< Јудина 1 >
1 Од Јуде, Исуса Христа слуге, а брата Јаковљевог, званима, који су освећени Богом Оцем и одржани Исусом Христом:
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 Милост и мир и љубав да вам се умножи.
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 Љубазни! Старајући се једнако да вам пишем за опште ваше спасење, би ми потребно да вам пишем молећи да се борите за праведну веру, која је једанпут дана светима.
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 Јер се увукоше неки безбожни људи, који су давно одређени на ово суђење, и Бога нашег благодат претварају у нечистоту, и јединог Господара Бога и Господа нашег Исуса Христа одричу се.
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 Али ћу вам напоменути, кад и ви знате ово једанпут, да Господ избави народ из земље мисирске, потом погуби оне који не вероваше.
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 И анђеле који не држаше своје старешинство него оставише свој стан чува у вечним оковима под мраком за суд великог дана. (aïdios )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
7 Као што Содом и Гомор, и околни њихови градови, који су се прокурвали онако као и они, и ходили за другим месом, поставише се углед и муче се у вечном огњу: (aiōnios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
8 Тако дакле и ови што сањајући тело погане, а поглаварства се одричу, и на славу хуле.
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 А Михаило Арханђел, кад се препираше с ђаволом и говораше за Мојсијево тело, не смеше проклети суд да изговори, него рече: Господ нека ти запрети.
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 А ови хуле на оно што не знаду; а шта знаду по природи као неразумна животиња, у оном се распадају.
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 Тешко њима! Јер путем Каиновим пођоше и у превару Валамове плате падоше, и у буни Корејевој изгибоше.
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 Ово су они што погане ваше милостиње једући с вама без страха и гојећи се; облаци безводни, које ветрови разносе; јесенска дрвета неродљива, која су двапут умрла, и из корена ишчупана;
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 Бесни валови морски, који се пене својим срамотама, звезде лажне, којима се чува мрак вечне таме. (aiōn )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
14 Али и за овакве пророкова Енох, седми од Адама, говорећи: Гле, иде Господ с хиљадама светих анђела својих
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 Да учини суд свима, и да покара све безбожнике за сва њихова безбожна дела којима безбожност чинише, и за све ружне речи њихове које безбожни грешници говорише на Њ.
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 Ово су незадовољни викачи, који по жељама својим живе, и уста њихова говоре поносите речи, и за добитак гледају ко је ко.
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 А ви, љубазни, опомињите се речи које напред казаше апостоли Господа нашег Исуса Христа,
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 Јер вам казаше да ће у последње време постати ругачи, који ће ходити по својим жељама и безбожностима.
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 Ово су они што се одвајају (од јединости вере), и јесу телесни, који духа немају.
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 А ви, љубазни, назиђујте се својом светом вером, и молите се Богу Духом Светим.
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 И сами себе држите у љубави Божијој, чекајући милост Господа нашег Исуса Христа за живот вечни. (aiōnios )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
22 И тако разликујући једне милујте.
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 А једне страхом избављајте и из огња вадите; а карајте са страхом, мрзећи и на хаљину опогањену од тела.
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 А Ономе који вас може сачувати без греха и без мане, и поставити праве пред славом својом у радости,
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 Једином премудром Богу и Спасу нашем, кроз Исуса Христа Господа нашег, слава и величанство, држава и власт пре свију векова и сад и у све векове. Амин. (aiōn )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )