< 1 Reis 9 >
1 Quando Salomão terminou a construção da casa de Yahweh, a casa do rei, e todo o desejo de Salomão que ele tinha o prazer de fazer,
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
2 Yahweh apareceu a Salomão pela segunda vez, como ele tinha aparecido a ele em Gibeon.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
3 Yahweh disse-lhe: “Ouvi sua oração e sua súplica que você fez diante de mim”. Fiz santa esta casa, que você construiu, para colocar meu nome lá para sempre; e meus olhos e meu coração estarão lá perpetuamente”.
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
4 Quanto a ti, se andares diante de mim como andou Davi, teu pai, em integridade de coração e retidão, para fazer conforme tudo o que te ordenei, e guardar meus estatutos e minhas ordenanças,
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
5 então estabelecerei o trono de teu reino sobre Israel para sempre, como prometi a Davi, teu pai, dizendo: “Não faltará de ti um homem no trono de Israel”.
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
6 Mas, se você se afastar de me seguir, você ou seus filhos, e não guardar meus mandamentos e meus estatutos que eu lhe propus, mas for e servir a outros deuses e adorá-los,
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
7 então eu cortarei Israel da terra que lhes dei; e lançarei fora da minha vista esta casa, que eu santificei pelo meu nome; e Israel será um provérbio e uma palavra de ordem entre todos os povos.
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
8 Though esta casa é tão alta, mas todos que passarem por ela ficarão espantados e assobiarão; e dirão: 'Por que Javé fez isto a esta terra e a esta casa?
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
9 e responderão: 'Porque abandonaram Javé seu Deus, que tirou seus pais da terra do Egito, e abraçaram outros deuses, e os adoraram, e os serviram. Portanto Yahweh trouxe todo este mal sobre eles””.
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
10 Ao final de vinte anos, nos quais Salomão tinha construído as duas casas, a casa de Yahweh e a casa do rei
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
11 (agora Hiram, o rei de Tiro, tinha mobiliado Salomão com cedros e ciprestes, e com ouro, de acordo com todo seu desejo), o rei Salomão deu a Hirão vinte cidades na terra da Galiléia.
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
12 Hirão saiu de Tiro para ver as cidades que Salomão lhe havia dado; e elas não lhe agradaram.
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
13 Ele disse: “Que cidades são essas que você me deu, meu irmão?”. Ele as chamou de terra de Cabul até os dias de hoje.
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
14 Hiram enviou ao rei cento e vinte talentos de ouro.
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
15 Esta é a razão do trabalho forçado que o rei Salomão recrutou: para construir a casa de Yahweh, sua própria casa, Millo, o muro de Jerusalém, Hazor, Megiddo, e Gezer.
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16 O Faraó rei do Egito subiu, tomou Gezer, queimou-a com fogo, matou os cananeus que viviam na cidade e a deu de presente de casamento a sua filha, a esposa de Salomão.
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
17 Salomão construiu na terra Gezer, Beth Horon a mais baixa,
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18 Baalath, Tamar no deserto,
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19 todas as cidades de armazenamento que Salomão tinha, as cidades para suas carruagens, as cidades para seus cavaleiros, e aquilo que Salomão desejava construir para seu prazer em Jerusalém, e no Líbano, e em toda a terra de seu domínio.
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
20 Quanto a todas as pessoas que ficaram dos amoritas, dos hititas, dos perizitas, dos hivitas e dos jebuseus, que não eram dos filhos de Israel -
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
21 seus filhos que foram deixados atrás deles na terra, que os filhos de Israel não puderam destruir totalmente - deles Salomão levantou até hoje uma taxa de servidão.
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
22 Mas dos filhos de Israel, Salomão não fez escravos; mas eles eram os homens de guerra, seus servos, seus príncipes, seus capitães e governantes de seus carros e de seus cavaleiros.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
23 Estes eram os quinhentos e cinqüenta oficiais chefes que estavam sobre o trabalho de Salomão, que governavam sobre o povo que trabalhava no trabalho.
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
24 Mas a filha do Faraó saiu da cidade de Davi para sua casa que Salomão havia construído para ela. Depois ele construiu Millo.
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
25 Salomão ofereceu holocaustos e ofertas de paz no altar que ele construiu para Iavé três vezes por ano, queimando incenso com eles no altar que estava antes de Iavé. Assim, ele terminou a casa.
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
26 O rei Salomão fez uma frota de navios em Ezion Geber, que fica ao lado de Eloth, na costa do Mar Vermelho, na terra de Edom.
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
27 Hiram enviou para a frota seus servos, marinheiros que tinham conhecimento do mar, com os servos de Salomão.
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
28 Eles vieram a Ophir, e de lá buscaram ouro, quatrocentos e vinte talentos, e o trouxeram ao rei Salomão.
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.