< 1 Reis 8 >
1 Então Salomão reuniu os anciãos de Israel com todos os chefes das tribos, os príncipes das famílias dos pais dos filhos de Israel, ao rei Salomão em Jerusalém, para trazer a arca da aliança de Iavé para fora da cidade de Davi, que é Sião.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 Todos os homens de Israel se reuniram ao rei Salomão na festa no mês de Ethanim, que é o sétimo mês.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 Todos os anciãos de Israel vieram, e os sacerdotes pegaram a arca.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 Eles trouxeram a arca de Yahweh, a Tenda da Reunião e todos os vasos sagrados que estavam na Tenda. Os sacerdotes e os levitas os trouxeram para cima.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 O rei Salomão e toda a congregação de Israel, que estavam reunidos com ele, estavam com ele diante da arca, sacrificando ovelhas e gado que não podiam ser contados ou numerados por multidão.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 Os sacerdotes trouxeram a arca da aliança de Iavé para seu lugar, para o santuário interior da casa, para o lugar santíssimo, mesmo sob as asas dos querubins.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 Pois os querubins estenderam suas asas sobre o lugar da arca, e os querubins cobriram a arca e seus postes acima.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 Os postes eram tão longos que as extremidades dos postes eram vistas do lugar sagrado antes do santuário interior, mas não eram vistas do lado de fora. Eles estão lá até hoje.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Não havia nada na arca, exceto as duas tábuas de pedra que Moisés colocou lá em Horeb, quando Javé fez um pacto com os filhos de Israel, quando eles saíram da terra do Egito.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Quando os sacerdotes saíram do lugar santo, aconteceu que a nuvem encheu a casa de Iavé,
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 para que os sacerdotes não suportassem ministrar por causa da nuvem; pois a glória de Iavé encheu a casa de Iavé.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Então Salomão disse: “Yahweh disse que iria habitar na escuridão espessa”.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 I certamente construíram para você uma casa de morada, um lugar para você morar para sempre”.
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 O rei virou seu rosto e abençoou toda a assembléia de Israel; e toda a assembléia de Israel ficou de pé.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 Ele disse: “Bendito seja Javé, o Deus de Israel, que falou com sua boca a Davi, seu pai, e cumpriu com sua mão, dizendo:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 'Desde o dia em que tirei meu povo Israel do Egito, não escolhi nenhuma cidade de todas as tribos de Israel para construir uma casa, para que meu nome pudesse estar lá; mas escolhi Davi para estar acima de meu povo Israel'.
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 “Agora estava no coração de David meu pai construir uma casa para o nome de Iavé, o Deus de Israel.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 Mas Javé disse a David, meu pai: “Enquanto estava em seu coração construir uma casa para o meu nome, você fez bem que estava em seu coração”.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 No entanto, não construirás a casa; mas teu filho, que sairá do teu corpo, construirá a casa em meu nome”.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 Javé estabeleceu sua palavra que falou; pois me levantei no lugar de Davi, meu pai, e me sento no trono de Israel, como Javé prometeu, e construí a casa para o nome de Javé, o Deus de Israel.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 Aí estabeleci um lugar para a arca, na qual está o pacto de Iavé, que ele fez com nossos pais quando os tirou da terra do Egito”.
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Salomão apresentou-se diante do altar de Javé na presença de toda a assembléia de Israel, e estendeu suas mãos para o céu;
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 e disse: “Javé, o Deus de Israel, não há Deus como tu, no céu em cima, nem na terra em baixo; que mantém aliança e bondade amorosa com teus servos que caminham diante de ti de todo o coração;
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 que manteve com teu servo Davi, meu pai, o que lhe prometeste. Sim, falou com a boca e a cumpriu com a mão, como é hoje.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 Agora, portanto, que Javé, o Deus de Israel, cumpra com seu servo Davi, meu pai, o que lhe prometeu, dizendo: “Não faltará de você um homem à minha vista para sentar-se no trono de Israel, se apenas seus filhos tomarem cuidado no seu caminho, para caminharem diante de mim como você caminhou diante de mim”.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 “Agora, portanto, Deus de Israel, por favor, permita que sua palavra seja verificada, a qual você falou com seu servo David, meu pai.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 Mas será que Deus habitará sobre a terra? Eis que o céu e o céu dos céus não te podem conter; quanto menos esta casa que eu construí!
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Mas respeita a oração de teu servo e sua súplica, Javé meu Deus, para ouvir o grito e a oração que teu servo faz hoje diante de ti;
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 para que teus olhos estejam abertos para esta casa noite e dia, mesmo para o lugar do qual disseste: “Meu nome estará ali;” para ouvir a oração que teu servo faz para este lugar.
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 Ouça a súplica de seu servo, e de seu povo Israel, quando rezarem em direção a este lugar. Sim, ouça no céu, seu lugar de morada; e quando ouvir, perdoe.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 “Se um homem pecar contra seu próximo, e lhe for feito um juramento para fazê-lo jurar, e ele vier e jurar diante de seu altar nesta casa,
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 então ouça no céu, e aja, e julgue seus servos, condenando os ímpios, para trazer seu caminho sobre sua própria cabeça, e justificando os justos, para dar-lhe de acordo com sua justiça.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 “Quando seu povo Israel for atingido diante do inimigo por ter pecado contra você, se eles se voltarem novamente para você e confessarem seu nome, e orarem e fizerem súplicas a você nesta casa,
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 então ouça no céu, e perdoe o pecado de seu povo Israel, e os traga novamente para a terra que você deu a seus pais.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 “Quando o céu estiver fechado e não houver chuva porque eles pecaram contra você, se orarem para este lugar e confessarem seu nome, e se voltarem do pecado deles quando você os afligir,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 então ouça no céu, e perdoe o pecado de seus servos, e de seu povo Israel, quando você lhes ensinar o bom caminho em que devem andar; e envie chuva em sua terra que você deu ao seu povo por herança.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 “Se houver fome na terra, se houver peste, se houver ferrugem, míldio, gafanhoto ou lagarta; se seu inimigo os sitiar na terra de suas cidades, qualquer que seja a praga, qualquer que seja a doença,
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 qualquer que seja a oração e súplica feita por qualquer homem, ou por todo seu povo Israel, que conhecerá cada um a praga de seu próprio coração, e estenderá suas mãos para esta casa,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 então ouça no céu, sua morada, e perdoe, e aja, e dê a cada homem de acordo com todos os seus caminhos, cujo coração você conhece (para você, até mesmo você só, conhece o coração de todos os filhos dos homens);
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 para que eles possam temer-te todos os dias que viverem na terra que deste a nossos pais.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 “Além disso, em relação ao estrangeiro, que não é do seu povo Israel, quando ele sair de um país distante por causa do seu nome
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 (pois eles ouvirão do seu grande nome e da sua mão poderosa e do seu braço estendido), quando ele vier e rezar para esta casa,
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 ouça no céu, seu lugar de residência, e faça de acordo com tudo o que o estrangeiro chamar por você; para que todos os povos da terra saibam seu nome, para temê-lo, assim como seu povo Israel, e para que saibam que esta casa que construí é chamada pelo seu nome.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 “Se seu povo sair para lutar contra seu inimigo, por qualquer caminho que você os envie, e eles rezarem a Javé para a cidade que você escolheu, e para a casa que eu construí para seu nome,
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 então ouça no céu sua oração e sua súplica, e mantenha sua causa.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 se pecarem contra ti (pois não há homem que não peque), e tu te indignares com eles e os entregares ao inimigo, para que os levem cativos para a terra do inimigo, longe ou perto;
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 yet se eles se arrependerem na terra onde são levados cativos, e se voltarem novamente, e te suplicarem na terra daqueles que os levaram cativos, dizendo: 'Nós pecamos e fizemos perversamente'; procedemos perversamente',
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 se eles voltarem a ti de todo o coração e com toda a alma na terra dos seus inimigos que os levaram cativos, e rezarem a ti para a terra deles que deste a seus pais, a cidade que escolheste e a casa que construí para o teu nome,
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 então ouve a oração deles e a súplica deles no céu, tua morada, e mantém a causa deles;
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 e perdoa teu povo que pecou contra ti, e todas as suas transgressões em que transgrediram contra ti; e dá-lhes compaixão diante daqueles que os levaram cativos, para que tenham compaixão deles
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 (pois eles são teu povo e tua herança, que tiraste do Egito, do meio do forno de ferro);
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 para que teus olhos estejam abertos à súplica de teu servo e à súplica de teu povo Israel, para escutá-los sempre que clamarem a ti.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 para que os separeis de todos os povos da terra para serem vossa herança, como falastes por Moisés vosso servo, quando trouxestes nossos pais para fora do Egito, Senhor Javé”.
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 Foi assim que, quando Salomão terminou de rezar toda esta oração e súplica a Javé, ele se levantou de diante do altar de Javé, de joelhos com as mãos estendidas para o céu.
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 Ele se levantou e abençoou toda a assembléia de Israel com uma voz alta, dizendo:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 “Bendito seja Javé, que deu descanso a seu povo Israel, de acordo com tudo o que ele prometeu. Não faltou uma palavra de toda sua boa promessa, que ele prometeu por Moisés, seu servo.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 Que Javé, nosso Deus, esteja conosco como estava com nossos pais. Que ele não nos deixe ou nos abandone,
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 para que ele incline nossos corações para ele, para caminhar em todos os seus caminhos, e para guardar seus mandamentos, seus estatutos e suas ordenanças, que ele ordenou a nossos pais.
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 Que estas minhas palavras, com as quais fiz súplicas diante de Javé, estejam perto de Javé nosso Deus dia e noite, para que ele possa manter a causa de seu servo e a causa de seu povo Israel, como todo dia exige;
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 para que todos os povos da terra saibam que o próprio Javé é Deus. Não há mais ninguém.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 “Que seu coração seja, portanto, perfeito com Javé nosso Deus, para andar em seus estatutos e guardar seus mandamentos, como é hoje”.
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 O rei, e todo Israel com ele, ofereceram sacrifício diante de Iavé.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 Salomão ofereceu pelo sacrifício de ofertas de paz, que ele ofereceu a Iavé, vinte e duas mil cabeças de gado e cento e vinte mil ovelhas. Assim, o rei e todos os filhos de Israel dedicaram a casa de Iavé.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 No mesmo dia o rei tornou sagrado o meio da corte que estava diante da casa de Iavé; pois ali ele ofereceu o holocausto, a oferta de refeição e a gordura das ofertas pacíficas, porque o altar de bronze que estava diante de Iavé era muito pequeno para receber o holocausto, a oferta de refeição e a gordura das ofertas pacíficas.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Então Salomão realizou a festa naquela época, e todo Israel com ele, uma grande assembléia, desde a entrada de Hamath até o riacho do Egito, diante de Iavé nosso Deus, sete dias e mais sete dias, mesmo catorze dias.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 No oitavo dia ele mandou o povo embora; e eles abençoaram o rei, e foram para suas tendas alegres e alegres em seus corações por toda a bondade que Javé havia mostrado a Davi, seu servo, e a Israel, seu povo.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.