< 11 >

1 Então respondeu Sofar, o naamathita, e disse
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Porventura não se dará resposta á multidão de palavras? E o homen fallador será justificado?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 A's tuas mentiras se hão de calar os homens? E zombarás tu sem que ninguem te envergonhe?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 Pois tu disseste: A minha doutrina é pura, e limpo sou aos teus olhos.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 Mas, na verdade, oxalá que Deus fallasse e abrisse os seus labios contra ti!
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 E te fizesse saber os segredos da sabedoria, que ella é multiplice em efficacia; pelo que sabe que Deus exige de ti menos do que merece a tua iniquidade.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Porventura alcançarás os caminhos de Deus? ou chegarás á perfeição do Todo-poderoso?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 Como as alturas dos céus é a sua sabedoria; que poderás tu fazer? mais profunda do que o inferno, que poderás tu saber? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 Mais comprida é a sua medida do que a terra: e mais larga do que o mar.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 Se elle destruir, e encerrar, ou se recolher, quem o fará tornar para traz?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 Porque elle conhece aos homens vãos, e vê o vicio; e não o terá em consideração?
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 Mas o homem vão é falto de entendimento; sim, o homem nasce como a cria do jumento montez.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 Se tu preparaste o teu coração, e estendeste as tuas mãos para elle!
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 Se ha iniquidade na tua mão, lança-a para longe de ti e não deixes habitar a injustiça nas tuas tendas.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Porque então o teu rosto levantarás sem macula: e estarás firme, e não temerás.
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Porque te esquecerás dos trabalhos, e te lembrarás d'elles como das aguas que já passaram
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 E a tua vida mais clara se levantará do que o meio dia; ainda que seja trevas, será como a manhã.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 E terás confiança; porque haverá esperança; e buscarás e repousarás seguro.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 E deitar-te-has, e ninguem te espantará; muitos supplicarão o teu rosto.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 Porém os olhos dos impios desfallecerão, e perecerá o seu refugio: e a sua esperança será o expirar da alma
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< 11 >