< Jó 10 >
1 A minha alma tem tedio á minha vida: darei livre curso á minha queixa, fallarei na amargura da minha alma.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 Direi a Deus: Não me condemnes: faze-me saber porque contendes comigo.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 Parece-te bem que me opprimas? que rejeites o trabalho das tuas mãos? e resplandeças sobre o conselho dos impios?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 Tens tu porventura olhos de carne? vês tu como vê o homem?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 São os teus dias como os dias do homem? Ou são os teus annos como os annos de um homem,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 Para te informares da minha iniquidade, e averiguares o meu peccado?
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 Bem sabes tu que eu não sou impio: todavia ninguem ha que me livre da tua mão.
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 As tuas mãos me fizeram e me formaram todo em roda; comtudo me consomes.
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Peço-te que te lembres de que como barro me formaste e me farás tornar em pó.
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 Porventura não me vasaste como leite, e como queijo me não coalhaste?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 De pelle e carne me vestiste, e com ossos e nervos me ligaste.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 Vida e beneficencia me fizeste: e o teu cuidado guardou o meu espirito.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 Porém estas coisas as occultaste no teu coração: bem sei eu que isto esteve comtigo.
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 Se eu peccar, tu me observas; e da minha iniquidade não me escusarás.
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 Se fôr impio, ai de mim! e se fôr justo, não levantarei a minha cabeça: farto estou de affronta; e olho para a minha miseria.
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 Porque se vae crescendo; tu me caças como a um leão feroz: tornas-te, e fazes maravilhas contra mim.
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 Tu renovas contra mim as tuas testemunhas, e multiplicas contra mim a tua ira; revezes e combate estão comigo.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 Por quepois me tiraste da madre? Ah se então dera o espirito, e olhos nenhuns me vissem!
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 Que tivera sido como se nunca fôra: e desde o ventre fôra levado á sepultura!
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 Porventura não são poucos os meus dias? cessa pois, e deixa-me, para que por um pouco eu tome alento;
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 Antes que vá e d'onde nunca torne, á terra da escuridão e da sombra da morte;
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 Terra escurissima, como a mesma escuridão, terra da sombra, da morte e sem ordem alguma e onde a luz é como a escuridão.
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”