< مزامیر 118 >

خداوند را حمد گویید زیرا که نیکوست و رحمت او تا ابدالاباداست. ۱ 1
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
اسرائیل بگویند که «رحمت او تا ابدالاباداست.» ۲ 2
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
خاندان هارون بگویند که «رحمت او تاابدالاباد است.» ۳ 3
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
ترسندگان خداوند بگویند که «رحمت او تا ابدالاباد است.» ۴ 4
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
در تنگی یاه را خواندم. یاه مرا اجابت فرموده، در جای وسیع آورد. ۵ 5
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
خداوند با من است، پس نخواهم ترسید. انسان به من چه تواندکرد؟ ۶ 6
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
خداوند برایم از مددکاران من است. پس من بر نفرت کنندگان خود آرزوی خویش راخواهم دید. ۷ 7
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
به خداوند پناه بردن بهتر است ازتوکل نمودن بر آدمیان. ۸ 8
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
به خداوند پناه بردن بهتراست از توکل نمودن بر امیران. ۹ 9
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
جمیع امتها مرااحاطه کردند، لیکن به نام خداوند ایشان را هلاک خواهم کرد. ۱۰ 10
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
مرا احاطه کردند و دور مراگرفتند، لیکن به نام خداوند ایشان را هلاک خواهم کرد. ۱۱ 11
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
مثل زنبورها مرا احاطه کردند ومثل آتش خارها خاموش شدند. زیرا که به نام خداوند ایشان را هلاک خواهم کرد. ۱۲ 12
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
بر من سخت هجوم آوردی تا بیفتم، لیکن خداوند مرااعانت نمود. ۱۳ 13
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
خداوند قوت و سرود من است ونجات من شده است. ۱۴ 14
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
آواز ترنم و نجات درخیمه های عادلان است. دست راست خداوند باشجاعت عمل می‌کند. ۱۵ 15
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
دست راست خداوندمتعال است. دست راست خداوند با شجاعت عمل می‌کند. ۱۶ 16
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
نمی میرم بلکه زیست خواهم کرد و کارهای یاه را ذکر خواهم نمود. ۱۷ 17
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
یاه مرابه شدت تنبیه نموده، لیکن مرا به موت نسپرده است. ۱۸ 18
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
دروازه های عدالت را برای من بگشایید! به آنها داخل شده، یاه را حمد خواهم گفت. ۱۹ 19
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
دروازه خداوند این است. عادلان بدان داخل خواهند شد. ۲۰ 20
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
تو را حمد می‌گویم زیرا که مرااجابت فرموده و نجات من شده‌ای. ۲۱ 21
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
سنگی راکه معماران رد کردند، همان سر زاویه شده است. ۲۲ 22
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
این از جانب خداوند شده و در نظر ما عجیب است. ۲۳ 23
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
این است روزی که خداوند ظاهر کرده است. درآن وجد و شادی خواهیم نمود. ۲۴ 24
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
آه‌ای خداوند نجات ببخش! آه‌ای خداوند سعادت عطا فرما! ۲۵ 25
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
متبارک باد او که به نام خداوندمی آید. شما را از خانه خداوند برکت می‌دهیم. ۲۶ 26
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
یهوه خدایی است که ما را روشن ساخته است. ذبیحه را به ریسمانها بر شاخهای قربانگاه ببندید. ۲۷ 27
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
تو خدای من هستی تو، پس تو را حمدمی گویم. خدای من، تو را متعال خواهم خواند. ۲۸ 28
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
خداوند را حمد گویید زیرا که نیکوست ورحمت او تا ابدالاباد است. ۲۹ 29
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< مزامیر 118 >